Selected

Original Text
Abubakar Gumi

Available Translations

83 Al-Muţaffifīn ٱلْمُطَفِّفِين

< Previous   36 Āyah   The Defrauding      Next >  

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.

83:1 وَيْلٌ لِّلْمُطَفِّفِينَ
83:1
Abubakar Gumi (Hausa) :
Bone ya tabbata ga mãsu naƙƙasãwa.

83:2 ٱلَّذِينَ إِذَا ٱكْتَالُوا۟ عَلَى ٱلنَّاسِ يَسْتَوْفُونَ
83:2
Abubakar Gumi (Hausa) :
Waɗanda suke idan suka auna daga mutãne suna cika mũdu.

83:3 وَإِذَا كَالُوهُمْ أَو وَّزَنُوهُمْ يُخْسِرُونَ
83:3
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma idan sun auna musu da zakka ko da sikẽli, suna ragẽwa

83:4 أَلَا يَظُنُّ أُو۟لَـٰٓئِكَ أَنَّهُم مَّبْعُوثُونَ
83:4
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ashe! Waɗancan bã su tabbata cẽwa lalle sũ, ana tãyar da su ba?

83:5 لِيَوْمٍ عَظِيمٍ
83:5
Abubakar Gumi (Hausa) :
Domin yini mai girma.

83:6 يَوْمَ يَقُومُ ٱلنَّاسُ لِرَبِّ ٱلْعَـٰلَمِينَ
83:6
Abubakar Gumi (Hausa) :
Yinin da mutãne ke tãshi zuwa ga Ubangijin halitta?

83:7 كَلَّآ إِنَّ كِتَـٰبَ ٱلْفُجَّارِ لَفِى سِجِّينٍ
83:7
Abubakar Gumi (Hausa) :
Haƙĩƙa lalle ne littãfin fãjirai dãhir, yana a cikin Sijjĩn.

83:8 وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا سِجِّينٌ
83:8
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma, mẽ ya sanar da kai abin da akẽ cẽ wa Sijjĩn?

83:9 كِتَـٰبٌ مَّرْقُومٌ
83:9
Abubakar Gumi (Hausa) :
Wani 1ittãfi ne rubũtacce.

83:10 وَيْلٌ يَوْمَئِذٍ لِّلْمُكَذِّبِينَ
83:10
Abubakar Gumi (Hausa) :
Bone yã tabbata a rãnar nan ga mãsu ƙaryatãwa.

83:11 ٱلَّذِينَ يُكَذِّبُونَ بِيَوْمِ ٱلدِّينِ
83:11
Abubakar Gumi (Hausa) :
Waɗanda suke ƙaryatãwa game da rãnar sakamako.

83:12 وَمَا يُكَذِّبُ بِهِۦٓ إِلَّا كُلُّ مُعْتَدٍ أَثِيمٍ
83:12
Abubakar Gumi (Hausa) :
Babũ mai ƙaryatãwa gare shi fãce dukan mai ƙẽtare haddi mai yawan zunubi.

83:13 إِذَا تُتْلَىٰ عَلَيْهِ ءَايَـٰتُنَا قَالَ أَسَـٰطِيرُ ٱلْأَوَّلِينَ
83:13
Abubakar Gumi (Hausa) :
Idan ana karãtun ãyõyinmu, a kansa, sai ya ce: tãtsũniyõyin mutãnen farko ne.

83:14 كَلَّا ۖ بَلْ ۜ رَانَ عَلَىٰ قُلُوبِهِم مَّا كَانُوا۟ يَكْسِبُونَ
83:14
Abubakar Gumi (Hausa) :
A'aha! Bã haka ba, abin da suka kasance suna aikatãwa dai, yã yi tsãtsa a cikin zukãtãnsu.

83:15 كَلَّآ إِنَّهُمْ عَن رَّبِّهِمْ يَوْمَئِذٍ لَّمَحْجُوبُونَ
83:15
Abubakar Gumi (Hausa) :
A'aha! Haƙĩƙa, lalle ne sũ daga Ubangijinsu, rãnar nan, waɗanda ake shãmakancẽwa ne.

83:16 ثُمَّ إِنَّهُمْ لَصَالُوا۟ ٱلْجَحِيمِ
83:16
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan, lalle ne, sũ mãsu shiga cikin Jahĩm ne.

83:17 ثُمَّ يُقَالُ هَـٰذَا ٱلَّذِى كُنتُم بِهِۦ تُكَذِّبُونَ
83:17
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan a ce: "Wannan shi ne abin da kuka kasance kuna ƙaryatãwa game da shi."

83:18 كَلَّآ إِنَّ كِتَـٰبَ ٱلْأَبْرَارِ لَفِى عِلِّيِّينَ
83:18
Abubakar Gumi (Hausa) :
A'aha! Haƙĩƙa lalle ne littãfin mãsu ɗã'ã yana a cikin Illiyyĩna?

83:19 وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا عِلِّيُّونَ
83:19
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma mẽne ne yã sanar da kai abin da ake cẽwa Illiyyũna?

83:20 كِتَـٰبٌ مَّرْقُومٌ
83:20
Abubakar Gumi (Hausa) :
Wani littãfi ne rubũtacce.

83:21 يَشْهَدُهُ ٱلْمُقَرَّبُونَ
83:21
Abubakar Gumi (Hausa) :
Muƙarrabai suke halarta shi.

83:22 إِنَّ ٱلْأَبْرَارَ لَفِى نَعِيمٍ
83:22
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne, mãsu ɗã'ã ga Allah tabbas suna cikin ni'ima.

83:23 عَلَى ٱلْأَرَآئِكِ يَنظُرُونَ
83:23
Abubakar Gumi (Hausa) :
A kan karagu, suna ta kallo.

83:24 تَعْرِفُ فِى وُجُوهِهِمْ نَضْرَةَ ٱلنَّعِيمِ
83:24
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kana sani a cikin huskõkinsu, akwai kwarjinin ni'ima.

83:25 يُسْقَوْنَ مِن رَّحِيقٍ مَّخْتُومٍ
83:25
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ana shãyar da sũ daga wata giya wadda aka yunƙe a kan rufinta.

83:26 خِتَـٰمُهُۥ مِسْكٌ ۚ وَفِى ذَٰلِكَ فَلْيَتَنَافَسِ ٱلْمُتَنَـٰفِسُونَ
83:26
Abubakar Gumi (Hausa) :
¡arshen kurɓinta miski ne. To, a cikin wannan, mãsu gwagwarmaya su yi ta gwagwarmayar nẽma.

83:27 وَمِزَاجُهُۥ مِن تَسْنِيمٍ
83:27
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma abin da ake gauraya ta da shi, daga tasnĩm yake.

83:28 عَيْنًا يَشْرَبُ بِهَا ٱلْمُقَرَّبُونَ
83:28
Abubakar Gumi (Hausa) :
(Wato) wani marmaro ne wanda muƙarrabai ke sha daga gare shi.

83:29 إِنَّ ٱلَّذِينَ أَجْرَمُوا۟ كَانُوا۟ مِنَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ يَضْحَكُونَ
83:29
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne, waɗanda suka kãfirta sun kasance (a dũniya) suna yi wa waɗanda suka yi ĩmãni dãriya.

83:30 وَإِذَا مَرُّوا۟ بِهِمْ يَتَغَامَزُونَ
83:30
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma idan sun shuɗe su sai su dinga yin zunɗe.

83:31 وَإِذَا ٱنقَلَبُوٓا۟ إِلَىٰٓ أَهْلِهِمُ ٱنقَلَبُوا۟ فَكِهِينَ
83:31
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma idan suka jũya zuwa ga iyãlansu, sai su tafi suna kãkãci.

83:32 وَإِذَا رَأَوْهُمْ قَالُوٓا۟ إِنَّ هَـٰٓؤُلَآءِ لَضَآلُّونَ
83:32
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma idan sun gan su sai su ce: "Lalle waɗannan ɓatattu ne."

83:33 وَمَآ أُرْسِلُوا۟ عَلَيْهِمْ حَـٰفِظِينَ
83:33
Abubakar Gumi (Hausa) :
Alhãli kuwa, ba a aike su ba dõmin su zama mãsu tsaro a kansu.

83:34 فَٱلْيَوْمَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ مِنَ ٱلْكُفَّارِ يَضْحَكُونَ
83:34
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, yau fa (a Lãhira] waɗanda suka yi ĩmãni, sũ ke yi wa kãfirai dãriya.

83:35 عَلَى ٱلْأَرَآئِكِ يَنظُرُونَ
83:35
Abubakar Gumi (Hausa) :
A kan karagu, suna ta kallo.

83:36 هَلْ ثُوِّبَ ٱلْكُفَّارُ مَا كَانُوا۟ يَفْعَلُونَ
83:36
Abubakar Gumi (Hausa) :
Shin an sãka ma kãfirai abin da suka kasance suna aikatawa?