Selected
                        Original Text
                        
                    
                
                    
                        Abubakar Gumi
                        
                        
                        
                    
                
                Abdullah Yusuf Ali
Abdul Majid Daryabadi
Abul Ala Maududi
Ahmed Ali
Ahmed Raza Khan
A. J. Arberry
Ali Quli Qarai
Hasan al-Fatih Qaribullah and Ahmad Darwish
Mohammad Habib Shakir
Mohammed Marmaduke William Pickthall
Muhammad Sarwar
Muhammad Taqi-ud-Din al-Hilali and Muhammad Muhsin Khan
Safi-ur-Rahman al-Mubarakpuri
Saheeh International
Talal Itani
Transliteration
Wahiduddin Khan
                    بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
                
                
                    In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.
                
            
                    83:1
                    وَيْلٌ لِّلْمُطَفِّفِينَ
                
                
                
                
                
                    83:1
                    Bone ya tabbata ga mãsu naƙƙasãwa.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    83:2
                    ٱلَّذِينَ إِذَا ٱكْتَالُوا۟ عَلَى ٱلنَّاسِ يَسْتَوْفُونَ
                
                
                
                
                
                    83:2
                    Waɗanda suke idan suka auna daga mutãne suna cika mũdu.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    83:3
                    وَإِذَا كَالُوهُمْ أَو وَّزَنُوهُمْ يُخْسِرُونَ
                
                
                
                
                
                    83:3
                    Kuma idan sun auna musu da zakka ko da sikẽli, suna ragẽwa  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    83:4
                    أَلَا يَظُنُّ أُو۟لَـٰٓئِكَ أَنَّهُم مَّبْعُوثُونَ
                
                
                
                
                
                    83:4
                    Ashe! Waɗancan bã su tabbata cẽwa lalle sũ, ana tãyar da su ba?  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    83:5
                    لِيَوْمٍ عَظِيمٍ
                
                
                
                
                
                    83:5
                    Domin yini mai girma.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    83:6
                    يَوْمَ يَقُومُ ٱلنَّاسُ لِرَبِّ ٱلْعَـٰلَمِينَ
                
                
                
                
                
                    83:6
                    Yinin da mutãne ke tãshi zuwa ga Ubangijin halitta?  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    83:7
                    كَلَّآ إِنَّ كِتَـٰبَ ٱلْفُجَّارِ لَفِى سِجِّينٍ
                
                
                
                
                
                    83:7
                    Haƙĩƙa lalle ne littãfin fãjirai dãhir, yana a cikin Sijjĩn.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    83:8
                    وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا سِجِّينٌ
                
                
                
                
                
                    83:8
                    Kuma, mẽ ya sanar da kai abin da akẽ cẽ wa Sijjĩn?  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    83:9
                    كِتَـٰبٌ مَّرْقُومٌ
                
                
                
                
                
                    83:9
                    Wani 1ittãfi ne rubũtacce.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    83:10
                    وَيْلٌ يَوْمَئِذٍ لِّلْمُكَذِّبِينَ
                
                
                
                
                
                    83:10
                    Bone yã tabbata a rãnar nan ga mãsu ƙaryatãwa.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    83:11
                    ٱلَّذِينَ يُكَذِّبُونَ بِيَوْمِ ٱلدِّينِ
                
                
                
                
                
                    83:11
                    Waɗanda suke ƙaryatãwa game da rãnar sakamako.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    83:12
                    وَمَا يُكَذِّبُ بِهِۦٓ إِلَّا كُلُّ مُعْتَدٍ أَثِيمٍ
                
                
                
                
                
                    83:12
                    Babũ mai ƙaryatãwa gare shi fãce dukan mai ƙẽtare haddi mai yawan zunubi.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    83:13
                    إِذَا تُتْلَىٰ عَلَيْهِ ءَايَـٰتُنَا قَالَ أَسَـٰطِيرُ ٱلْأَوَّلِينَ
                
                
                
                
                
                    83:13
                    Idan ana karãtun ãyõyinmu, a kansa, sai ya ce: tãtsũniyõyin mutãnen farko ne.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    83:14
                    كَلَّا ۖ بَلْ ۜ رَانَ عَلَىٰ قُلُوبِهِم مَّا كَانُوا۟ يَكْسِبُونَ
                
                
                
                
                
                    83:14
                    A'aha! Bã haka ba, abin da suka kasance suna aikatãwa dai, yã yi tsãtsa a cikin zukãtãnsu.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    83:15
                    كَلَّآ إِنَّهُمْ عَن رَّبِّهِمْ يَوْمَئِذٍ لَّمَحْجُوبُونَ
                
                
                
                
                
                    83:15
                    A'aha! Haƙĩƙa, lalle ne sũ daga Ubangijinsu, rãnar nan, waɗanda ake shãmakancẽwa ne.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    83:16
                    ثُمَّ إِنَّهُمْ لَصَالُوا۟ ٱلْجَحِيمِ
                
                
                
                
                
                    83:16
                    Sa'an nan, lalle ne, sũ mãsu shiga cikin Jahĩm ne.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    83:17
                    ثُمَّ يُقَالُ هَـٰذَا ٱلَّذِى كُنتُم بِهِۦ تُكَذِّبُونَ
                
                
                
                
                
                    83:17
                    Sa'an nan a ce: "Wannan shi ne abin da kuka kasance kuna ƙaryatãwa game da shi."  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    83:18
                    كَلَّآ إِنَّ كِتَـٰبَ ٱلْأَبْرَارِ لَفِى عِلِّيِّينَ
                
                
                
                
                
                    83:18
                    A'aha! Haƙĩƙa lalle ne littãfin mãsu ɗã'ã yana a cikin Illiyyĩna?  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    83:19
                    وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا عِلِّيُّونَ
                
                
                
                
                
                    83:19
                    Kuma mẽne ne yã sanar da kai abin da ake cẽwa Illiyyũna?  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    83:20
                    كِتَـٰبٌ مَّرْقُومٌ
                
                
                
                
                
                    83:20
                    Wani littãfi ne rubũtacce.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    83:21
                    يَشْهَدُهُ ٱلْمُقَرَّبُونَ
                
                
                
                
                
                    83:21
                    Muƙarrabai suke halarta shi.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    83:22
                    إِنَّ ٱلْأَبْرَارَ لَفِى نَعِيمٍ
                
                
                
                
                
                    83:22
                    Lalle ne, mãsu ɗã'ã ga Allah tabbas suna cikin ni'ima.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    83:23
                    عَلَى ٱلْأَرَآئِكِ يَنظُرُونَ
                
                
                
                
                
                    83:23
                    A kan karagu, suna ta kallo.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    83:24
                    تَعْرِفُ فِى وُجُوهِهِمْ نَضْرَةَ ٱلنَّعِيمِ
                
                
                
                
                
                    83:24
                    Kana sani a cikin huskõkinsu, akwai kwarjinin ni'ima.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    83:25
                    يُسْقَوْنَ مِن رَّحِيقٍ مَّخْتُومٍ
                
                
                
                
                
                    83:25
                    Ana shãyar da sũ daga wata giya wadda aka yunƙe a kan rufinta.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    83:26
                    خِتَـٰمُهُۥ مِسْكٌ ۚ وَفِى ذَٰلِكَ فَلْيَتَنَافَسِ ٱلْمُتَنَـٰفِسُونَ
                
                
                
                
                
                    83:26
                    ¡arshen kurɓinta miski ne. To, a cikin wannan, mãsu gwagwarmaya su yi ta gwagwarmayar nẽma.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    83:27
                    وَمِزَاجُهُۥ مِن تَسْنِيمٍ
                
                
                
                
                
                    83:27
                    Kuma abin da ake gauraya ta da shi, daga tasnĩm yake.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    83:28
                    عَيْنًا يَشْرَبُ بِهَا ٱلْمُقَرَّبُونَ
                
                
                
                
                
                    83:28
                    (Wato) wani marmaro ne wanda muƙarrabai ke sha daga gare shi.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    83:29
                    إِنَّ ٱلَّذِينَ أَجْرَمُوا۟ كَانُوا۟ مِنَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ يَضْحَكُونَ
                
                
                
                
                
                    83:29
                    Lalle ne, waɗanda suka kãfirta sun kasance (a dũniya) suna yi wa waɗanda suka yi ĩmãni dãriya.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    83:30
                    وَإِذَا مَرُّوا۟ بِهِمْ يَتَغَامَزُونَ
                
                
                
                
                
                    83:30
                    Kuma idan sun shuɗe su sai su dinga yin zunɗe.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    83:31
                    وَإِذَا ٱنقَلَبُوٓا۟ إِلَىٰٓ أَهْلِهِمُ ٱنقَلَبُوا۟ فَكِهِينَ
                
                
                
                
                
                    83:31
                    Kuma idan suka jũya zuwa ga iyãlansu, sai su tafi suna kãkãci.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    83:32
                    وَإِذَا رَأَوْهُمْ قَالُوٓا۟ إِنَّ هَـٰٓؤُلَآءِ لَضَآلُّونَ
                
                
                
                
                
                    83:32
                    Kuma idan sun gan su sai su ce: "Lalle waɗannan ɓatattu ne."  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    83:33
                    وَمَآ أُرْسِلُوا۟ عَلَيْهِمْ حَـٰفِظِينَ
                
                
                
                
                
                    83:33
                    Alhãli kuwa, ba a aike su ba dõmin su zama mãsu tsaro a kansu.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    83:34
                    فَٱلْيَوْمَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ مِنَ ٱلْكُفَّارِ يَضْحَكُونَ
                
                
                
                
                
                    83:34
                    To, yau fa (a Lãhira] waɗanda suka yi ĩmãni, sũ ke yi wa kãfirai dãriya.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    83:35
                    عَلَى ٱلْأَرَآئِكِ يَنظُرُونَ
                
                
                
                
                
                    83:35
                    A kan karagu, suna ta kallo.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    83:36
                    هَلْ ثُوِّبَ ٱلْكُفَّارُ مَا كَانُوا۟ يَفْعَلُونَ
                
                
                
                
                
                    83:36
                    Shin an sãka ma kãfirai abin da suka kasance suna aikatawa?  - Abubakar Gumi (Hausa)