Selected

Original Text
Abubakar Gumi

Available Translations

86 Aţ-Ţāriq ٱلطَّارِق

< Previous   17 Āyah   The Nightcommer      Next >  

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.

86:1 وَٱلسَّمَآءِ وَٱلطَّارِقِ
86:1
Abubakar Gumi (Hausa) :
Inã rantsuwa da sama da mai aukõwa da dare.

86:2 وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا ٱلطَّارِقُ
86:2
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, mẽ yã sanar da kai abin da ake cẽwa mai aukõwa da dare?

86:3 ٱلنَّجْمُ ٱلثَّاقِبُ
86:3
Abubakar Gumi (Hausa) :
Shi ne taurãron nan mai tsananin haske.

86:4 إِن كُلُّ نَفْسٍ لَّمَّا عَلَيْهَا حَافِظٌ
86:4
Abubakar Gumi (Hausa) :
Bãbu wani rai fãce a kansa akwai wani mai tsaro.

86:5 فَلْيَنظُرِ ٱلْإِنسَـٰنُ مِمَّ خُلِقَ
86:5
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, mutum ya dũba, daga mẽ aka halittã shi?

86:6 خُلِقَ مِن مَّآءٍ دَافِقٍ
86:6
Abubakar Gumi (Hausa) :
An halittã shi daga wani ruwa mai tunkuɗar jũna.

86:7 يَخْرُجُ مِنۢ بَيْنِ ٱلصُّلْبِ وَٱلتَّرَآئِبِ
86:7
Abubakar Gumi (Hausa) :
Yanã fita daga tsakanin tsatso da karankarman ƙirji.

86:8 إِنَّهُۥ عَلَىٰ رَجْعِهِۦ لَقَادِرٌ
86:8
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne Shi (Allah), ga mayar da shi (mutum), tabbas Mai iyãwa ne.

86:9 يَوْمَ تُبْلَى ٱلسَّرَآئِرُ
86:9
Abubakar Gumi (Hausa) :
Rãnar da ake jarrabawar asirai.

86:10 فَمَا لَهُۥ مِن قُوَّةٍ وَلَا نَاصِرٍ
86:10
Abubakar Gumi (Hausa) :
Saboda haka, bã shi da wani ƙarfi, kuma bã shi da wani mai taimako (da zai iya kãre shi daga azãbar Allah).

86:11 وَٱلسَّمَآءِ ذَاتِ ٱلرَّجْعِ
86:11
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ina rantsuwa da sama ma'abũciyar ruwa mai kõmãwa yana yankẽwa.

86:12 وَٱلْأَرْضِ ذَاتِ ٱلصَّدْعِ
86:12
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da ƙasa ma'abũciyar tsãgẽwa,

86:13 إِنَّهُۥ لَقَوْلٌ فَصْلٌ
86:13
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne shĩ (Alƙur'ãni), haƙĩƙa magana ce daki-daki

86:14 وَمَا هُوَ بِٱلْهَزْلِ
86:14
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma shĩ bã bananci bane

86:15 إِنَّهُمْ يَكِيدُونَ كَيْدًا
86:15
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne sũ, suna ƙulla kaidi na sõsai.

86:16 وَأَكِيدُ كَيْدًا
86:16
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma Ni, Ina mayar da kaidi (gare su) kamar yadda suke ƙulla kaidi.

86:17 فَمَهِّلِ ٱلْكَـٰفِرِينَ أَمْهِلْهُمْ رُوَيْدًۢا
86:17
Abubakar Gumi (Hausa) :
Saboda haka, ka yi wa kafirai jinkiri, ka dakata musu, sannu-sannu.