Selected

Original Text
Abubakar Gumi

Available Translations

96 Al-`Alaq ٱلْعَلَق

< Previous   19 Āyah   The Clot      Next >  

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.

96:1 ٱقْرَأْ بِٱسْمِ رَبِّكَ ٱلَّذِى خَلَقَ
96:1
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ka yi karatu da sunan Ubangijinka, wanda Ya yi halitta.

96:2 خَلَقَ ٱلْإِنسَـٰنَ مِنْ عَلَقٍ
96:2
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ya hahitta mutum daga gudan jini.

96:3 ٱقْرَأْ وَرَبُّكَ ٱلْأَكْرَمُ
96:3
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ka yi karatu, kuma UbangiJinka shi ne Mafi karimci.

96:4 ٱلَّذِى عَلَّمَ بِٱلْقَلَمِ
96:4
Abubakar Gumi (Hausa) :
Wanda Ya sanar (da mutum) game da alƙalami.

96:5 عَلَّمَ ٱلْإِنسَـٰنَ مَا لَمْ يَعْلَمْ
96:5
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ya sanar da mutum abin da bai sani ba.

96:6 كَلَّآ إِنَّ ٱلْإِنسَـٰنَ لَيَطْغَىٰٓ
96:6
Abubakar Gumi (Hausa) :
A'aha! Lalle, ne mutum haƙĩƙa, yana girman kai (ya ƙi karatu).

96:7 أَن رَّءَاهُ ٱسْتَغْنَىٰٓ
96:7
Abubakar Gumi (Hausa) :
Dõmin yã ga kansa, yã wadãta.

96:8 إِنَّ إِلَىٰ رَبِّكَ ٱلرُّجْعَىٰٓ
96:8
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne zuwa ga Ubangijinka makoma take.

96:9 أَرَءَيْتَ ٱلَّذِى يَنْهَىٰ
96:9
Abubakar Gumi (Hausa) :
Shin, kã ga wanda ke hana.

96:10 عَبْدًا إِذَا صَلَّىٰٓ
96:10
Abubakar Gumi (Hausa) :
Bãwã idan yã yi salla?

96:11 أَرَءَيْتَ إِن كَانَ عَلَى ٱلْهُدَىٰٓ
96:11
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ashe, kã gani, idan (shi bãwan) ya kasance a kan shiriya?

96:12 أَوْ أَمَرَ بِٱلتَّقْوَىٰٓ
96:12
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ko ya yi umurni da taƙawa?

96:13 أَرَءَيْتَ إِن كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰٓ
96:13
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ashe, kã gani, idan (shi mai hanin) ya ƙaryata, kuma ya jũya bãya?

96:14 أَلَمْ يَعْلَم بِأَنَّ ٱللَّهَ يَرَىٰ
96:14
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ashe, bai sani ba cewa Allah Yanã gani?

96:15 كَلَّا لَئِن لَّمْ يَنتَهِ لَنَسْفَعًۢا بِٱلنَّاصِيَةِ
96:15
Abubakar Gumi (Hausa) :
A'aha! Lalle ne, idan bai hanu ba, lalle ne zã Mu ja gãshin makwarkwaɗa.

96:16 نَاصِيَةٍ كَـٰذِبَةٍ خَاطِئَةٍ
96:16
Abubakar Gumi (Hausa) :
Makwarkwaɗa maƙaryaciya, mai laifi.

96:17 فَلْيَدْعُ نَادِيَهُۥ
96:17
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai ya kirayi ƙungiyarsa.

96:18 سَنَدْعُ ٱلزَّبَانِيَةَ
96:18
Abubakar Gumi (Hausa) :
Zã Mu kirayi zabaniyãwa (mala'iku mãsu girma).

96:19 كَلَّا لَا تُطِعْهُ وَٱسْجُدْ وَٱقْتَرِب ۩
96:19
Abubakar Gumi (Hausa) :
A'aha kada ka bĩ shi. Kuma ka yi tawali'u, kuma ka nemi kusanta (zuwa ga Ubangijinka).