Selected
Original Text
Abubakar Gumi
Abdullah Yusuf Ali
Abdul Majid Daryabadi
Abul Ala Maududi
Ahmed Ali
Ahmed Raza Khan
A. J. Arberry
Ali Quli Qarai
Hasan al-Fatih Qaribullah and Ahmad Darwish
Mohammad Habib Shakir
Mohammed Marmaduke William Pickthall
Muhammad Sarwar
Muhammad Taqi-ud-Din al-Hilali and Muhammad Muhsin Khan
Safi-ur-Rahman al-Mubarakpuri
Saheeh International
Talal Itani
Transliteration
Wahiduddin Khan
بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.
90:1
لَآ أُقْسِمُ بِهَـٰذَا ٱلْبَلَدِ
90:1
Bã sai Na yi rantsuwa da wannan gari ba. - Abubakar Gumi (Hausa)
90:2
وَأَنتَ حِلٌّۢ بِهَـٰذَا ٱلْبَلَدِ
90:2
Alhãli kai kanã mai sauka a cikin wannan gari. - Abubakar Gumi (Hausa)
90:3
وَوَالِدٍ وَمَا وَلَدَ
90:3
Da mahaifi da abin da ya haifa. - Abubakar Gumi (Hausa)
90:4
لَقَدْ خَلَقْنَا ٱلْإِنسَـٰنَ فِى كَبَدٍ
90:4
Lalle ne, Mun halitta mutum cikin wahala. - Abubakar Gumi (Hausa)
90:5
أَيَحْسَبُ أَن لَّن يَقْدِرَ عَلَيْهِ أَحَدٌ
90:5
Kõ yanã zaton bãbu wani mai iya sãmun iko, a kansa? - Abubakar Gumi (Hausa)
90:6
يَقُولُ أَهْلَكْتُ مَالًا لُّبَدًا
90:6
Yana cẽwa "Na halakarda dũkiya mai yawa," - Abubakar Gumi (Hausa)
90:7
أَيَحْسَبُ أَن لَّمْ يَرَهُۥٓ أَحَدٌ
90:7
Shin, yana zaton cewa wani bai gan shi ba? - Abubakar Gumi (Hausa)
90:8
أَلَمْ نَجْعَل لَّهُۥ عَيْنَيْنِ
90:8
Shin, ba Mu sanya masa idãnu biyu ba? - Abubakar Gumi (Hausa)
90:9
وَلِسَانًا وَشَفَتَيْنِ
90:9
Da harshe, da leɓɓa biyu. - Abubakar Gumi (Hausa)
90:10
وَهَدَيْنَـٰهُ ٱلنَّجْدَيْنِ
90:10
Kuma ba Mu shiryar da shi ga hanyõyi biyu ba? - Abubakar Gumi (Hausa)
90:11
فَلَا ٱقْتَحَمَ ٱلْعَقَبَةَ
90:11
To, don mene ne bai shiga Aƙabã ba? - Abubakar Gumi (Hausa)
90:12
وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا ٱلْعَقَبَةُ
90:12
Kuma mene ne ya sanar da kai abin da ake cẽ wa Aƙabã? - Abubakar Gumi (Hausa)
90:13
فَكُّ رَقَبَةٍ
90:13
Ita ce fansar wuyan bãwa. - Abubakar Gumi (Hausa)
90:14
أَوْ إِطْعَـٰمٌ فِى يَوْمٍ ذِى مَسْغَبَةٍ
90:14
Ko kuwa ciyarwa, a cikin yini ma'abũcin yunwa. - Abubakar Gumi (Hausa)
90:15
يَتِيمًا ذَا مَقْرَبَةٍ
90:15
Ga marãya ma'abũcin zumunta. - Abubakar Gumi (Hausa)
90:16
أَوْ مِسْكِينًا ذَا مَتْرَبَةٍ
90:16
Ko kuwa wani matalauci ma'abũcin turɓãya. - Abubakar Gumi (Hausa)
90:17
ثُمَّ كَانَ مِنَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ وَتَوَاصَوْا۟ بِٱلصَّبْرِ وَتَوَاصَوْا۟ بِٱلْمَرْحَمَةِ
90:17
Sa'an nan kuma ya kasance daga waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka yi wa jũna wasiyya da yin haƙuri, kuma suka yi wa jũna wasiyya da tausayi. - Abubakar Gumi (Hausa)
90:18
أُو۟لَـٰٓئِكَ أَصْحَـٰبُ ٱلْمَيْمَنَةِ
90:18
Waɗannan ne ma'abũta albarka - Abubakar Gumi (Hausa)
90:19
وَٱلَّذِينَ كَفَرُوا۟ بِـَٔايَـٰتِنَا هُمْ أَصْحَـٰبُ ٱلْمَشْـَٔمَةِ
90:19
Kuma waɗanda suka kãfirta da ãyõyinMu, sũ ne ma'abũta shu'umci - Abubakar Gumi (Hausa)
90:20
عَلَيْهِمْ نَارٌ مُّؤْصَدَةٌۢ
90:20
A kansu akwai wata wuta abar kullewa. - Abubakar Gumi (Hausa)