Selected
Original Text
Abubakar Gumi
Abdullah Yusuf Ali
Abdul Majid Daryabadi
Abul Ala Maududi
Ahmed Ali
Ahmed Raza Khan
A. J. Arberry
Ali Quli Qarai
Hasan al-Fatih Qaribullah and Ahmad Darwish
Mohammad Habib Shakir
Mohammed Marmaduke William Pickthall
Muhammad Sarwar
Muhammad Taqi-ud-Din al-Hilali and Muhammad Muhsin Khan
Safi-ur-Rahman al-Mubarakpuri
Saheeh International
Talal Itani
Transliteration
Wahiduddin Khan
بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.
70:1
سَأَلَ سَآئِلٌۢ بِعَذَابٍ وَاقِعٍ
70:1
Wani mai tambaya yã yi tambaya game da azãba, mai aukuwa. - Abubakar Gumi (Hausa)
70:2
لِّلْكَـٰفِرِينَ لَيْسَ لَهُۥ دَافِعٌ
70:2
Ga kãfirai, bã ta da mai tunkuɗẽwa. - Abubakar Gumi (Hausa)
70:3
مِّنَ ٱللَّهِ ذِى ٱلْمَعَارِجِ
70:3
Daga Allah Mai matãkala. - Abubakar Gumi (Hausa)
70:4
تَعْرُجُ ٱلْمَلَـٰٓئِكَةُ وَٱلرُّوحُ إِلَيْهِ فِى يَوْمٍ كَانَ مِقْدَارُهُۥ خَمْسِينَ أَلْفَ سَنَةٍ
70:4
Malã'iku da Ruhi (Jibrila) sunã tãkãwa zuwa gare Shi, a cikin yini wanda gwargwadonsa, shẽkara dubu hamsin ne. - Abubakar Gumi (Hausa)
70:5
فَٱصْبِرْ صَبْرًا جَمِيلًا
70:5
Sabõda haka, ka yi haƙuri, haƙuri mai kyãwo. - Abubakar Gumi (Hausa)
70:6
إِنَّهُمْ يَرَوْنَهُۥ بَعِيدًا
70:6
Lalle ne su, sunã ganin ta mai nĩsa. - Abubakar Gumi (Hausa)
70:7
وَنَرَىٰهُ قَرِيبًا
70:7
Kuma Mu, Muna ganin ta a kusa. - Abubakar Gumi (Hausa)
70:8
يَوْمَ تَكُونُ ٱلسَّمَآءُ كَٱلْمُهْلِ
70:8
Rãnar da sama zã ta kasance kamar narkakkar azurfa. - Abubakar Gumi (Hausa)
70:9
وَتَكُونُ ٱلْجِبَالُ كَٱلْعِهْنِ
70:9
Kuma duwãtsu su zama kamar saɓin sũfi. - Abubakar Gumi (Hausa)
70:10
وَلَا يَسْـَٔلُ حَمِيمٌ حَمِيمًا
70:10
Kuma abõki bã ya tambayar inda wani abõki yake. - Abubakar Gumi (Hausa)
70:11
يُبَصَّرُونَهُمْ ۚ يَوَدُّ ٱلْمُجْرِمُ لَوْ يَفْتَدِى مِنْ عَذَابِ يَوْمِئِذٍۭ بِبَنِيهِ
70:11
Ana sanya su, su gajũna, mai laifi na gũrin dã zai iya yin fansa, daga azãbar rãnar nan, da ɗiyansa, - Abubakar Gumi (Hausa)
70:12
وَصَـٰحِبَتِهِۦ وَأَخِيهِ
70:12
Da matarsa da ɗan'uwansa. - Abubakar Gumi (Hausa)
70:13
وَفَصِيلَتِهِ ٱلَّتِى تُـْٔوِيهِ
70:13
Da danginsa, mãsu tattarã shi. - Abubakar Gumi (Hausa)
70:14
وَمَن فِى ٱلْأَرْضِ جَمِيعًا ثُمَّ يُنجِيهِ
70:14
Da wanda ke a cikin dũniya duka gabã ɗaya, sa'an nan fansar, ta tsĩrar da shi. - Abubakar Gumi (Hausa)
70:15
كَلَّآ ۖ إِنَّهَا لَظَىٰ
70:15
A'aha! Lalle ne fa, ita ce Lazã, - Abubakar Gumi (Hausa)
70:16
نَزَّاعَةً لِّلشَّوَىٰ
70:16
Mai twãle fãtar goshi. - Abubakar Gumi (Hausa)
70:17
تَدْعُوا۟ مَنْ أَدْبَرَ وَتَوَلَّىٰ
70:17
Tanã kiran wanda ya jũya bãya (daga addini) kuma ya kau da kai. - Abubakar Gumi (Hausa)
70:18
وَجَمَعَ فَأَوْعَىٰٓ
70:18
Ya tãra (dũkiya), kuma ya sanya ta a cikin jaka. - Abubakar Gumi (Hausa)
70:19
۞ إِنَّ ٱلْإِنسَـٰنَ خُلِقَ هَلُوعًا
70:19
Lalle ne mutum an halitta shi mai ciwon kwaɗayi. - Abubakar Gumi (Hausa)
70:20
إِذَا مَسَّهُ ٱلشَّرُّ جَزُوعًا
70:20
Idan sharri ya shãfe shi, ya kãsa haƙuri. - Abubakar Gumi (Hausa)
70:21
وَإِذَا مَسَّهُ ٱلْخَيْرُ مَنُوعًا
70:21
Kuma idan alhẽri ya shãfe shi, ya yi rõwa. - Abubakar Gumi (Hausa)
70:22
إِلَّا ٱلْمُصَلِّينَ
70:22
Sai mãsu yin salla, - Abubakar Gumi (Hausa)
70:23
ٱلَّذِينَ هُمْ عَلَىٰ صَلَاتِهِمْ دَآئِمُونَ
70:23
Waɗanda suke, a kan sallarsu, su, mãsu dawwama ne. - Abubakar Gumi (Hausa)
70:24
وَٱلَّذِينَ فِىٓ أَمْوَٰلِهِمْ حَقٌّ مَّعْلُومٌ
70:24
Kuma waɗanda a cikin dũkiyarsu, akwai wani haƙƙi sananne. - Abubakar Gumi (Hausa)
70:25
لِّلسَّآئِلِ وَٱلْمَحْرُومِ
70:25
Ga (matalauci) mai rõƙo da wanda aka hanã wa roƙon. - Abubakar Gumi (Hausa)
70:26
وَٱلَّذِينَ يُصَدِّقُونَ بِيَوْمِ ٱلدِّينِ
70:26
Da waɗannan da ke gaskata rãnar sakamako. - Abubakar Gumi (Hausa)
70:27
وَٱلَّذِينَ هُم مِّنْ عَذَابِ رَبِّهِم مُّشْفِقُونَ
70:27
Da waɗannan sabõda azãbar Ubangijinsu, suna jin tsõro. - Abubakar Gumi (Hausa)
70:28
إِنَّ عَذَابَ رَبِّهِمْ غَيْرُ مَأْمُونٍ
70:28
Lalle ne, azãbar Ubangijinsu bã wadda ake iya amincẽwaba ce. - Abubakar Gumi (Hausa)
70:29
وَٱلَّذِينَ هُمْ لِفُرُوجِهِمْ حَـٰفِظُونَ
70:29
Da waɗanda suke, ga farjojinsu, mãsu tsarewa ne. - Abubakar Gumi (Hausa)
70:30
إِلَّا عَلَىٰٓ أَزْوَٰجِهِمْ أَوْ مَا مَلَكَتْ أَيْمَـٰنُهُمْ فَإِنَّهُمْ غَيْرُ مَلُومِينَ
70:30
Sai fa a kan matan aurensu da abin da hannayensu na dãma suka mallaka. To lalle ne sũkam ba waɗanda ake zargi ba ne. - Abubakar Gumi (Hausa)
70:31
فَمَنِ ٱبْتَغَىٰ وَرَآءَ ذَٰلِكَ فَأُو۟لَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلْعَادُونَ
70:31
To, duk wanda ya nẽmi abin da yake a bayan wannan, to, waɗancan sũ ne mãsu ƙetare iyãka. - Abubakar Gumi (Hausa)
70:32
وَٱلَّذِينَ هُمْ لِأَمَـٰنَـٰتِهِمْ وَعَهْدِهِمْ رَٰعُونَ
70:32
Kuma da waɗannan da suke ga amãnõninsu da alkawarinsu mãsu tsarẽwa ne. - Abubakar Gumi (Hausa)
70:33
وَٱلَّذِينَ هُم بِشَهَـٰدَٰتِهِمْ قَآئِمُونَ
70:33
Kuma da waɗanda suke, ga shaidarsu, mãsu dãgẽwa ne. - Abubakar Gumi (Hausa)
70:34
وَٱلَّذِينَ هُمْ عَلَىٰ صَلَاتِهِمْ يُحَافِظُونَ
70:34
Kuma waɗanda suke, a kan sallarsu, mãsu tsarẽwa ne. - Abubakar Gumi (Hausa)
70:35
أُو۟لَـٰٓئِكَ فِى جَنَّـٰتٍ مُّكْرَمُونَ
70:35
Waɗannan, a cikin gidãjen Aljanna, waɗanda ake girmamãwa ne - Abubakar Gumi (Hausa)
70:36
فَمَالِ ٱلَّذِينَ كَفَرُوا۟ قِبَلَكَ مُهْطِعِينَ
70:36
Mẽ yã sãmi waɗanda suka kãfirta, a wajenka, sunã gaugãwar (gudu). - Abubakar Gumi (Hausa)
70:37
عَنِ ٱلْيَمِينِ وَعَنِ ٱلشِّمَالِ عِزِينَ
70:37
Daga jihar dãma, kuma daga jihar hagu, jama'a-jama'a! - Abubakar Gumi (Hausa)
70:38
أَيَطْمَعُ كُلُّ ٱمْرِئٍ مِّنْهُمْ أَن يُدْخَلَ جَنَّةَ نَعِيمٍ
70:38
Shin kõwane mutum daga cikinsu yana nẽman a shigar da shi a Aljannar ni'ima ne (ba da wani aiki ba)? - Abubakar Gumi (Hausa)
70:39
كَلَّآ ۖ إِنَّا خَلَقْنَـٰهُم مِّمَّا يَعْلَمُونَ
70:39
A'aha! Lalle Mũ, Mun halitta su, daga abin da suka sani. - Abubakar Gumi (Hausa)
70:40
فَلَآ أُقْسِمُ بِرَبِّ ٱلْمَشَـٰرِقِ وَٱلْمَغَـٰرِبِ إِنَّا لَقَـٰدِرُونَ
70:40
Sabõda haka ba sai Na yi rantsuwa da Ubangijin wurãren ɓullõwar rãna da wurãren fãɗuwarta ba, lalle Mũ, Mãsu iyãwa ne. - Abubakar Gumi (Hausa)
70:41
عَلَىٰٓ أَن نُّبَدِّلَ خَيْرًا مِّنْهُمْ وَمَا نَحْنُ بِمَسْبُوقِينَ
70:41
Ga Mu musanya waɗanda suke mafi alhẽri, daga gare su. Kuma ba Mu kasance waɗanda ake rinjãya ba. - Abubakar Gumi (Hausa)
70:42
فَذَرْهُمْ يَخُوضُوا۟ وَيَلْعَبُوا۟ حَتَّىٰ يُلَـٰقُوا۟ يَوْمَهُمُ ٱلَّذِى يُوعَدُونَ
70:42
Sabõda haka ka bar su, su dulmuya, kuma su yi wãsã, har su haɗu da rãnarsu wadda ake yi musu alkawari (da ita). - Abubakar Gumi (Hausa)
70:43
يَوْمَ يَخْرُجُونَ مِنَ ٱلْأَجْدَاثِ سِرَاعًا كَأَنَّهُمْ إِلَىٰ نُصُبٍ يُوفِضُونَ
70:43
Rãnar da suke fitowa daga kaburbura da gaugãwa, kamar sũ, zuwa ga wata kafaffiyar (tuta), suke yin gaugãwa. - Abubakar Gumi (Hausa)
70:44
خَـٰشِعَةً أَبْصَـٰرُهُمْ تَرْهَقُهُمْ ذِلَّةٌ ۚ ذَٰلِكَ ٱلْيَوْمُ ٱلَّذِى كَانُوا۟ يُوعَدُونَ
70:44
Maƙaskanta ga idanunsu, wani walakanci yana rufe su. wannan shi ne yinin da suka kasance ana yi musa alkawari (a kansa.) - Abubakar Gumi (Hausa)