Selected

Original Text
Abubakar Gumi

Available Translations

89 Al-Fajr ٱلْفَجْر

< Previous   30 Āyah   The Dawn      Next >  

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.

89:1 وَٱلْفَجْرِ
89:1
Abubakar Gumi (Hausa) :
Inã rantsuwa da alfijiri.

89:2 وَلَيَالٍ عَشْرٍ
89:2
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da darũruwa gõma.

89:3 وَٱلشَّفْعِ وَٱلْوَتْرِ
89:3
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da (adadi na) cikã da (na) mãrã.

89:4 وَٱلَّيْلِ إِذَا يَسْرِ
89:4
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da dare idan yana shũɗewa.

89:5 هَلْ فِى ذَٰلِكَ قَسَمٌ لِّذِى حِجْرٍ
89:5
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ko a cikin waɗannan akwai abin rantsuwa ga mai hankali (da yake kange shi daga zunubi)?

89:6 أَلَمْ تَرَ كَيْفَ فَعَلَ رَبُّكَ بِعَادٍ
89:6
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ba ka ga yadda Ubangijinka Ya aikata da Ãdãwa ba?

89:7 إِرَمَ ذَاتِ ٱلْعِمَادِ
89:7
Abubakar Gumi (Hausa) :
Iramawa mãsu sakon ƙĩrar jiki.

89:8 ٱلَّتِى لَمْ يُخْلَقْ مِثْلُهَا فِى ٱلْبِلَـٰدِ
89:8
Abubakar Gumi (Hausa) :
Waɗanda ba a halitta kwatankwacinsu ba a cikin garũruwa (na dũniya).

89:9 وَثَمُودَ ٱلَّذِينَ جَابُوا۟ ٱلصَّخْرَ بِٱلْوَادِ
89:9
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da samũdãwa waɗanda suka fasa duwãtsu a cikin Wadi suka yi gidãje)?

89:10 وَفِرْعَوْنَ ذِى ٱلْأَوْتَادِ
89:10
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da Fir'auna mai turãku.

89:11 ٱلَّذِينَ طَغَوْا۟ فِى ٱلْبِلَـٰدِ
89:11
Abubakar Gumi (Hausa) :
Waɗanda suka ƙẽtare iyãkarsu, a cikin garũruwa?

89:12 فَأَكْثَرُوا۟ فِيهَا ٱلْفَسَادَ
89:12
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sabõda haka, suka yawaita yin ɓarna a cikinsu.

89:13 فَصَبَّ عَلَيْهِمْ رَبُّكَ سَوْطَ عَذَابٍ
89:13
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sabõda haka Ubangijinka Ya zuba musu bũlãlar azãba.

89:14 إِنَّ رَبَّكَ لَبِٱلْمِرْصَادِ
89:14
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne, Ubangijinka Yana nan a mafaka.

89:15 فَأَمَّا ٱلْإِنسَـٰنُ إِذَا مَا ٱبْتَلَىٰهُ رَبُّهُۥ فَأَكْرَمَهُۥ وَنَعَّمَهُۥ فَيَقُولُ رَبِّىٓ أَكْرَمَنِ
89:15
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, amma fa mutum idan Ubangijibsa Ya jarraba shi, wãto Yã girmama shi kuma Ya yi masa ni'ima, sai ya ce: "Ubangijina Ya girmama ni."

89:16 وَأَمَّآ إِذَا مَا ٱبْتَلَىٰهُ فَقَدَرَ عَلَيْهِ رِزْقَهُۥ فَيَقُولُ رَبِّىٓ أَهَـٰنَنِ
89:16
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma idan Ya jarraba shi, wãto Ya ƙuntata masa abincinsa, sai ya ce: "Ubangijina Ya walãkanta ni."

89:17 كَلَّا ۖ بَل لَّا تُكْرِمُونَ ٱلْيَتِيمَ
89:17
Abubakar Gumi (Hausa) :
A'aha! Bari wannan, ai bã ku girmama marãya!

89:18 وَلَا تَحَـٰٓضُّونَ عَلَىٰ طَعَامِ ٱلْمِسْكِينِ
89:18
Abubakar Gumi (Hausa) :
Bã ku kwaɗaitã wa jũnanku ga (tattalin) abincin matalauci!

89:19 وَتَأْكُلُونَ ٱلتُّرَاثَ أَكْلًا لَّمًّا
89:19
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma kuna cin dũkiyar gãdo, ci na tãrãwa.

89:20 وَتُحِبُّونَ ٱلْمَالَ حُبًّا جَمًّا
89:20
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma kuna son dũkiya, so mai yawa.

89:21 كَلَّآ إِذَا دُكَّتِ ٱلْأَرْضُ دَكًّا دَكًّا
89:21
Abubakar Gumi (Hausa) :
A'aha! Idan aka niƙa ƙasa niƙewa sosai.

89:22 وَجَآءَ رَبُّكَ وَٱلْمَلَكُ صَفًّا صَفًّا
89:22
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma Ubangijinka Ya zo, alhãli malã'iku na jẽre, safũ- safu.

89:23 وَجِا۟ىٓءَ يَوْمَئِذٍۭ بِجَهَنَّمَ ۚ يَوْمَئِذٍ يَتَذَكَّرُ ٱلْإِنسَـٰنُ وَأَنَّىٰ لَهُ ٱلذِّكْرَىٰ
89:23
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma a ranar nan aka zo da Jahannama. A ranar nan mutum zai yi tunãni. To, inã fa tunãni yake a gare shi!

89:24 يَقُولُ يَـٰلَيْتَنِى قَدَّمْتُ لِحَيَاتِى
89:24
Abubakar Gumi (Hausa) :
Yana dinga cẽwa, "Kaitona, dã na gabatar (da aikin ƙwarai) domin rãyuwata!"

89:25 فَيَوْمَئِذٍ لَّا يُعَذِّبُ عَذَابَهُۥٓ أَحَدٌ
89:25
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, a rãnar nan bãbu wani mai yin azãba irin azãbar Allah.

89:26 وَلَا يُوثِقُ وَثَاقَهُۥٓ أَحَدٌ
89:26
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma bãbu wani mai ɗauri irin ɗaurinSa.

89:27 يَـٰٓأَيَّتُهَا ٱلنَّفْسُ ٱلْمُطْمَئِنَّةُ
89:27
Abubakar Gumi (Hausa) :
Yã kai rai mai natsuwa!

89:28 ٱرْجِعِىٓ إِلَىٰ رَبِّكِ رَاضِيَةً مَّرْضِيَّةً
89:28
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ka koma zuwa ga Ubangijinka, alhãli kana mai yarda (da abin da Ya ƙaddara maka a dũniya) abar yardarwa (da sakamakon da zã a ba ka a Lãhira).

89:29 فَٱدْخُلِى فِى عِبَـٰدِى
89:29
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sabõbda haka, ka shiga cikin bãyiNa (mãsu bin umurui a dũniya).

89:30 وَٱدْخُلِى جَنَّتِى
89:30
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma ka shiga AljannaTa (a Lãhira).