Selected

Original Text
Abubakar Gumi

Available Translations

69 Al-Ĥāqqah ٱلْحَاقَّة

< Previous   52 Āyah   The Reality      Next >  

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.

69:1 ٱلْحَآقَّةُ
69:1
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kiran gaskiya!

69:2 مَا ٱلْحَآقَّةُ
69:2
Abubakar Gumi (Hausa) :
Mẽne ne kiran gaskiya?

69:3 وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا ٱلْحَآقَّةُ
69:3
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽwa kiran gaskiya?

69:4 كَذَّبَتْ ثَمُودُ وَعَادٌۢ بِٱلْقَارِعَةِ
69:4
Abubakar Gumi (Hausa) :
Samũdãwa da Ãdãwa sun ƙaryatar da kiran gaskiya mai dũkar zũciya!

69:5 فَأَمَّا ثَمُودُ فَأُهْلِكُوا۟ بِٱلطَّاغِيَةِ
69:5
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, amma Samũdãwa to, an halakãsu da tsãwa mai tsanani.

69:6 وَأَمَّا عَادٌ فَأُهْلِكُوا۟ بِرِيحٍ صَرْصَرٍ عَاتِيَةٍ
69:6
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma amma Ãdãwa to, an halaka su da wata iska mai tsananin sauti wadda ta ƙẽtare haddi.

69:7 سَخَّرَهَا عَلَيْهِمْ سَبْعَ لَيَالٍ وَثَمَـٰنِيَةَ أَيَّامٍ حُسُومًا فَتَرَى ٱلْقَوْمَ فِيهَا صَرْعَىٰ كَأَنَّهُمْ أَعْجَازُ نَخْلٍ خَاوِيَةٍ
69:7
Abubakar Gumi (Hausa) :
(Allah) Ya hõre ta a kansu a cikin dare bakwai da yini takwas, biye da jũna, sabõda haka, kana ganin mutãne a cikinta kwance. Kamar sũ ƙirãruwan dabĩno ne, waɗanda suka fãɗi.

69:8 فَهَلْ تَرَىٰ لَهُم مِّنۢ بَاقِيَةٍ
69:8
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, kõ kanã ganin abin da ya yi saurã daga cikinsu?

69:9 وَجَآءَ فِرْعَوْنُ وَمَن قَبْلَهُۥ وَٱلْمُؤْتَفِكَـٰتُ بِٱلْخَاطِئَةِ
69:9
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma Fir'auna yã zo da waɗanda ke gabãninsa, da waɗannan da aka kife ƙasarsu, sabõda laifi.

69:10 فَعَصَوْا۟ رَسُولَ رَبِّهِمْ فَأَخَذَهُمْ أَخْذَةً رَّابِيَةً
69:10
Abubakar Gumi (Hausa) :
Dõmin sun sãɓã wa manzon Ubangijinsu, sabõda haka ya kãmã su da wani irin kãmu mai ƙãruwar (tsanani).

69:11 إِنَّا لَمَّا طَغَا ٱلْمَآءُ حَمَلْنَـٰكُمْ فِى ٱلْجَارِيَةِ
69:11
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne, Mũ, a lõkacin da ruwa ya ƙẽtare haddi, Munɗauke aaku a cikin jirgin ruwan nan.

69:12 لِنَجْعَلَهَا لَكُمْ تَذْكِرَةً وَتَعِيَهَآ أُذُنٌ وَٰعِيَةٌ
69:12
Abubakar Gumi (Hausa) :
Dõmin Mu sanya shi, gare ku abin tunãwa kuma wani kunne mai kiyayewa ya kiyaye (shi).

69:13 فَإِذَا نُفِخَ فِى ٱلصُّورِ نَفْخَةٌ وَٰحِدَةٌ
69:13
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, idan an yi bũsa a cikin ƙaho, bũsa ɗaya.

69:14 وَحُمِلَتِ ٱلْأَرْضُ وَٱلْجِبَالُ فَدُكَّتَا دَكَّةً وَٰحِدَةً
69:14
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma aka ɗauki ƙasa da duwãtsu, kuma aka niƙa su niƙãwa ɗaya.

69:15 فَيَوْمَئِذٍ وَقَعَتِ ٱلْوَاقِعَةُ
69:15
Abubakar Gumi (Hausa) :
A ran nan, mai aukuwa zã ta auku.

69:16 وَٱنشَقَّتِ ٱلسَّمَآءُ فَهِىَ يَوْمَئِذٍ وَاهِيَةٌ
69:16
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma sama zã ta tsãge, dõmin ita a ran nan, mai rauni ce.

69:17 وَٱلْمَلَكُ عَلَىٰٓ أَرْجَآئِهَا ۚ وَيَحْمِلُ عَرْشَ رَبِّكَ فَوْقَهُمْ يَوْمَئِذٍ ثَمَـٰنِيَةٌ
69:17
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma malã'iku (su bayyana) a kan sãsanninta, kuma wasu (malã'iku) takwas na ɗauke da Al'arshin Ubangijinka, a sama da su, a wannan rãnar.

69:18 يَوْمَئِذٍ تُعْرَضُونَ لَا تَخْفَىٰ مِنكُمْ خَافِيَةٌ
69:18
Abubakar Gumi (Hausa) :
A rãnar nan zã a bijirã ku (dõmin hisãbi), bãbu wani rai, mai ɓoyewa, daga cikinku, wanda zai iya ɓõyẽwa.

69:19 فَأَمَّا مَنْ أُوتِىَ كِتَـٰبَهُۥ بِيَمِينِهِۦ فَيَقُولُ هَآؤُمُ ٱقْرَءُوا۟ كِتَـٰبِيَهْ
69:19
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, amma wanda aka bai wa littãfinsa a dãmansa, sai ya ce wa (makusantansa), "Ku karɓa, ku karanta littafina."

69:20 إِنِّى ظَنَنتُ أَنِّى مُلَـٰقٍ حِسَابِيَهْ
69:20
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Lalle ne ni, nã tabbata cewa ni mai haɗuwa da hisãbina ne."

69:21 فَهُوَ فِى عِيشَةٍ رَّاضِيَةٍ
69:21
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sabõda haka, shi yana cikin wata rãyuwa yardadda.

69:22 فِى جَنَّةٍ عَالِيَةٍ
69:22
Abubakar Gumi (Hausa) :
A cikin Aljanna maɗaukakiya.

69:23 قُطُوفُهَا دَانِيَةٌ
69:23
Abubakar Gumi (Hausa) :
Nunannun 'yã'yan itãcenta makusantã ne (ga mai son ɗĩba),

69:24 كُلُوا۟ وَٱشْرَبُوا۟ هَنِيٓـًٔۢا بِمَآ أَسْلَفْتُمْ فِى ٱلْأَيَّامِ ٱلْخَالِيَةِ
69:24
Abubakar Gumi (Hausa) :
(Ana ce musu) "Ku ci, kuma ku sha a cikin ni'ima, sabõda abin da kuka gabãtar a cikin kwãnukan da suka shige."

69:25 وَأَمَّا مَنْ أُوتِىَ كِتَـٰبَهُۥ بِشِمَالِهِۦ فَيَقُولُ يَـٰلَيْتَنِى لَمْ أُوتَ كِتَـٰبِيَهْ
69:25
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma wanda aka bai wa littãfinsa ga hagunsa, sai ya ce: "Kaitona, ba a kãwo mini littãfina ba!"

69:26 وَلَمْ أَدْرِ مَا حِسَابِيَهْ
69:26
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma ban san abin da (ke sakamakon) hisãbina ba!"

69:27 يَـٰلَيْتَهَا كَانَتِ ٱلْقَاضِيَةَ
69:27
Abubakar Gumi (Hausa) :
"In dã dai ita, tã kasance mai halakã ni gabã ɗaya ce!

69:28 مَآ أَغْنَىٰ عَنِّى مَالِيَهْ ۜ
69:28
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Dukiyãta ba ta wadatar da ni ba!"

69:29 هَلَكَ عَنِّى سُلْطَـٰنِيَهْ
69:29
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Ĩkona ya ɓace mini!"

69:30 خُذُوهُ فَغُلُّوهُ
69:30
Abubakar Gumi (Hausa) :
(Sai a ce wa malã'iku) "Ku kãmã shi, sa'an nan ku sanyã shi a cikin ƙuƙumi."

69:31 ثُمَّ ٱلْجَحِيمَ صَلُّوهُ
69:31
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Sa'an nan, a cikin Jahĩm, ku ƙõna shi."

69:32 ثُمَّ فِى سِلْسِلَةٍ ذَرْعُهَا سَبْعُونَ ذِرَاعًا فَٱسْلُكُوهُ
69:32
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Sa'an nan, acikin sarƙa, tsawonta zirã'i saba'in, sai ku sanya shi."

69:33 إِنَّهُۥ كَانَ لَا يُؤْمِنُ بِٱللَّهِ ٱلْعَظِيمِ
69:33
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Lalle ne, shi ya kasance ba ya yin ĩmãni da Allah, Mai girma!"

69:34 وَلَا يَحُضُّ عَلَىٰ طَعَامِ ٱلْمِسْكِينِ
69:34
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma ba ya kwaɗaitarwa ga (bãyar da) abincin matalauci!"

69:35 فَلَيْسَ لَهُ ٱلْيَوْمَ هَـٰهُنَا حَمِيمٌ
69:35
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Sabõda haka, a yau, a nan, bã ya da masõyi."

69:36 وَلَا طَعَامٌ إِلَّا مِنْ غِسْلِينٍ
69:36
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma bãbu wani abinci, sai daga (itãcen) gislĩn."

69:37 لَّا يَأْكُلُهُۥٓ إِلَّا ٱلْخَـٰطِـُٔونَ
69:37
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Bãbu mai cin sa sai mãsu ganganci."

69:38 فَلَآ أُقْسِمُ بِمَا تُبْصِرُونَ
69:38
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, ba sai Nã yi rantsuwa da abin da kuke iya gani ba,

69:39 وَمَا لَا تُبْصِرُونَ
69:39
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da abin da bã ku iya gani.

69:40 إِنَّهُۥ لَقَوْلُ رَسُولٍ كَرِيمٍ
69:40
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne, shi (Alƙur'ani) tabbas maganar wani manzo (Jibirilu) mai daraja ne.

69:41 وَمَا هُوَ بِقَوْلِ شَاعِرٍ ۚ قَلِيلًا مَّا تُؤْمِنُونَ
69:41
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma shi ba maganar wani mawãƙi ba ne. Kaɗan ƙwarai zã ku gaskata.

69:42 وَلَا بِقَوْلِ كَاهِنٍ ۚ قَلِيلًا مَّا تَذَكَّرُونَ
69:42
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma bã maganar bõka ba ne. Kaɗan ƙwarai zã ku iya tunãwa.

69:43 تَنزِيلٌ مِّن رَّبِّ ٱلْعَـٰلَمِينَ
69:43
Abubakar Gumi (Hausa) :
Abin saukarwã ne daga Ubangijin halitta duka.

69:44 وَلَوْ تَقَوَّلَ عَلَيْنَا بَعْضَ ٱلْأَقَاوِيلِ
69:44
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma dã (Muhammadu) yã faɗi wata maganã, yã jingina ta garẽ Mu.

69:45 لَأَخَذْنَا مِنْهُ بِٱلْيَمِينِ
69:45
Abubakar Gumi (Hausa) :
Dã Mun kãma shi da dãma.

69:46 ثُمَّ لَقَطَعْنَا مِنْهُ ٱلْوَتِينَ
69:46
Abubakar Gumi (Hausa) :
sa'an nan, lalle ne, dã Mun kãtse masa lakã.

69:47 فَمَا مِنكُم مِّنْ أَحَدٍ عَنْهُ حَـٰجِزِينَ
69:47
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma daga cikinku bãbu wasu mãsu iya kãre (azãbarMu) daga gare shi.

69:48 وَإِنَّهُۥ لَتَذْكِرَةٌ لِّلْمُتَّقِينَ
69:48
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma lalle ne shi (Alƙur'ãni) tanãtarwa ce ga mãsu taƙawa.

69:49 وَإِنَّا لَنَعْلَمُ أَنَّ مِنكُم مُّكَذِّبِينَ
69:49
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma lalle, ne Mũ, wallahi Munã sane da cẽwa daga cikinku alwwai mãsu ƙaryatãwa.

69:50 وَإِنَّهُۥ لَحَسْرَةٌ عَلَى ٱلْكَـٰفِرِينَ
69:50
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma lalle ne shi (Alƙarãni) wallahi baƙin ciki ne ga kãfirai.

69:51 وَإِنَّهُۥ لَحَقُّ ٱلْيَقِينِ
69:51
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma lalle, ne shi gaskiya ce ta yaƙshẽni.

69:52 فَسَبِّحْ بِٱسْمِ رَبِّكَ ٱلْعَظِيمِ
69:52
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sabõda haka, ka tsarkake sũnan Ubangjinka, mai girma.