Selected
                        Original Text
                        
                    
                
                    
                        Abubakar Gumi
                        
                        
                        
                    
                
                Abdullah Yusuf Ali
Abdul Majid Daryabadi
Abul Ala Maududi
Ahmed Ali
Ahmed Raza Khan
A. J. Arberry
Ali Quli Qarai
Hasan al-Fatih Qaribullah and Ahmad Darwish
Mohammad Habib Shakir
Mohammed Marmaduke William Pickthall
Muhammad Sarwar
Muhammad Taqi-ud-Din al-Hilali and Muhammad Muhsin Khan
Safi-ur-Rahman al-Mubarakpuri
Saheeh International
Talal Itani
Transliteration
Wahiduddin Khan
                    بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
                
                
                    In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.
                
            
                    69:1
                    ٱلْحَآقَّةُ
                
                
                
                
                
                    69:1
                    Kiran gaskiya!  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:2
                    مَا ٱلْحَآقَّةُ
                
                
                
                
                
                    69:2
                    Mẽne ne kiran gaskiya?  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:3
                    وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا ٱلْحَآقَّةُ
                
                
                
                
                
                    69:3
                    Kuma mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽwa kiran gaskiya?  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:4
                    كَذَّبَتْ ثَمُودُ وَعَادٌۢ بِٱلْقَارِعَةِ
                
                
                
                
                
                    69:4
                    Samũdãwa da Ãdãwa sun ƙaryatar da kiran gaskiya mai dũkar zũciya!  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:5
                    فَأَمَّا ثَمُودُ فَأُهْلِكُوا۟ بِٱلطَّاغِيَةِ
                
                
                
                
                
                    69:5
                    To, amma Samũdãwa to, an halakãsu da tsãwa mai tsanani.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:6
                    وَأَمَّا عَادٌ فَأُهْلِكُوا۟ بِرِيحٍ صَرْصَرٍ عَاتِيَةٍ
                
                
                
                
                
                    69:6
                    Kuma amma Ãdãwa to, an halaka su da wata iska mai tsananin sauti wadda ta ƙẽtare haddi.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:7
                    سَخَّرَهَا عَلَيْهِمْ سَبْعَ لَيَالٍ وَثَمَـٰنِيَةَ أَيَّامٍ حُسُومًا فَتَرَى ٱلْقَوْمَ فِيهَا صَرْعَىٰ كَأَنَّهُمْ أَعْجَازُ نَخْلٍ خَاوِيَةٍ
                
                
                
                
                
                    69:7
                    (Allah) Ya hõre ta a kansu a cikin dare bakwai da yini takwas, biye da jũna, sabõda haka, kana ganin mutãne a cikinta kwance. Kamar sũ ƙirãruwan dabĩno ne, waɗanda suka fãɗi.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:8
                    فَهَلْ تَرَىٰ لَهُم مِّنۢ بَاقِيَةٍ
                
                
                
                
                
                    69:8
                    To, kõ kanã ganin abin da ya yi saurã daga cikinsu?  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:9
                    وَجَآءَ فِرْعَوْنُ وَمَن قَبْلَهُۥ وَٱلْمُؤْتَفِكَـٰتُ بِٱلْخَاطِئَةِ
                
                
                
                
                
                    69:9
                    Kuma Fir'auna yã zo da waɗanda ke gabãninsa, da waɗannan da aka kife ƙasarsu, sabõda laifi.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:10
                    فَعَصَوْا۟ رَسُولَ رَبِّهِمْ فَأَخَذَهُمْ أَخْذَةً رَّابِيَةً
                
                
                
                
                
                    69:10
                    Dõmin sun sãɓã wa manzon Ubangijinsu, sabõda haka ya kãmã su da wani irin kãmu mai ƙãruwar (tsanani).  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:11
                    إِنَّا لَمَّا طَغَا ٱلْمَآءُ حَمَلْنَـٰكُمْ فِى ٱلْجَارِيَةِ
                
                
                
                
                
                    69:11
                    Lalle ne, Mũ, a lõkacin da ruwa ya ƙẽtare haddi, Munɗauke aaku a cikin jirgin ruwan nan.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:12
                    لِنَجْعَلَهَا لَكُمْ تَذْكِرَةً وَتَعِيَهَآ أُذُنٌ وَٰعِيَةٌ
                
                
                
                
                
                    69:12
                    Dõmin Mu sanya shi, gare ku abin tunãwa kuma wani kunne mai kiyayewa ya kiyaye (shi).  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:13
                    فَإِذَا نُفِخَ فِى ٱلصُّورِ نَفْخَةٌ وَٰحِدَةٌ
                
                
                
                
                
                    69:13
                    To, idan an yi bũsa a cikin ƙaho, bũsa ɗaya.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:14
                    وَحُمِلَتِ ٱلْأَرْضُ وَٱلْجِبَالُ فَدُكَّتَا دَكَّةً وَٰحِدَةً
                
                
                
                
                
                    69:14
                    Kuma aka ɗauki ƙasa da duwãtsu, kuma aka niƙa su niƙãwa ɗaya.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:15
                    فَيَوْمَئِذٍ وَقَعَتِ ٱلْوَاقِعَةُ
                
                
                
                
                
                    69:15
                    A ran nan, mai aukuwa zã ta auku.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:16
                    وَٱنشَقَّتِ ٱلسَّمَآءُ فَهِىَ يَوْمَئِذٍ وَاهِيَةٌ
                
                
                
                
                
                    69:16
                    Kuma sama zã ta tsãge, dõmin ita a ran nan, mai rauni ce.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:17
                    وَٱلْمَلَكُ عَلَىٰٓ أَرْجَآئِهَا ۚ وَيَحْمِلُ عَرْشَ رَبِّكَ فَوْقَهُمْ يَوْمَئِذٍ ثَمَـٰنِيَةٌ
                
                
                
                
                
                    69:17
                    Kuma malã'iku (su bayyana) a kan sãsanninta, kuma wasu (malã'iku) takwas na ɗauke da Al'arshin Ubangijinka, a sama da su, a wannan rãnar.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:18
                    يَوْمَئِذٍ تُعْرَضُونَ لَا تَخْفَىٰ مِنكُمْ خَافِيَةٌ
                
                
                
                
                
                    69:18
                    A rãnar nan zã a bijirã ku (dõmin hisãbi), bãbu wani rai, mai ɓoyewa, daga cikinku, wanda zai iya ɓõyẽwa.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:19
                    فَأَمَّا مَنْ أُوتِىَ كِتَـٰبَهُۥ بِيَمِينِهِۦ فَيَقُولُ هَآؤُمُ ٱقْرَءُوا۟ كِتَـٰبِيَهْ
                
                
                
                
                
                    69:19
                    To, amma wanda aka bai wa littãfinsa a dãmansa, sai ya ce wa (makusantansa), "Ku karɓa, ku karanta littafina."  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:20
                    إِنِّى ظَنَنتُ أَنِّى مُلَـٰقٍ حِسَابِيَهْ
                
                
                
                
                
                    69:20
                    "Lalle ne ni, nã tabbata cewa ni mai haɗuwa da hisãbina ne."  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:21
                    فَهُوَ فِى عِيشَةٍ رَّاضِيَةٍ
                
                
                
                
                
                    69:21
                    Sabõda haka, shi yana cikin wata rãyuwa yardadda.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:22
                    فِى جَنَّةٍ عَالِيَةٍ
                
                
                
                
                
                    69:22
                    A cikin Aljanna maɗaukakiya.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:23
                    قُطُوفُهَا دَانِيَةٌ
                
                
                
                
                
                    69:23
                    Nunannun 'yã'yan itãcenta makusantã ne (ga mai son ɗĩba),  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:24
                    كُلُوا۟ وَٱشْرَبُوا۟ هَنِيٓـًٔۢا بِمَآ أَسْلَفْتُمْ فِى ٱلْأَيَّامِ ٱلْخَالِيَةِ
                
                
                
                
                
                    69:24
                    (Ana ce musu) "Ku ci, kuma ku sha a cikin ni'ima, sabõda abin da kuka gabãtar a cikin kwãnukan da suka shige."  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:25
                    وَأَمَّا مَنْ أُوتِىَ كِتَـٰبَهُۥ بِشِمَالِهِۦ فَيَقُولُ يَـٰلَيْتَنِى لَمْ أُوتَ كِتَـٰبِيَهْ
                
                
                
                
                
                    69:25
                    Kuma wanda aka bai wa littãfinsa ga hagunsa, sai ya ce: "Kaitona, ba a kãwo mini littãfina ba!"  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:26
                    وَلَمْ أَدْرِ مَا حِسَابِيَهْ
                
                
                
                
                
                    69:26
                    "Kuma ban san abin da (ke sakamakon) hisãbina ba!"  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:27
                    يَـٰلَيْتَهَا كَانَتِ ٱلْقَاضِيَةَ
                
                
                
                
                
                    69:27
                    "In dã dai ita, tã kasance mai halakã ni gabã ɗaya ce!  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:28
                    مَآ أَغْنَىٰ عَنِّى مَالِيَهْ ۜ
                
                
                
                
                
                    69:28
                    "Dukiyãta ba ta wadatar da ni ba!"  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:29
                    هَلَكَ عَنِّى سُلْطَـٰنِيَهْ
                
                
                
                
                
                    69:29
                    "Ĩkona ya ɓace mini!"  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:30
                    خُذُوهُ فَغُلُّوهُ
                
                
                
                
                
                    69:30
                    (Sai a ce wa malã'iku) "Ku kãmã shi, sa'an nan ku sanyã shi a cikin ƙuƙumi."  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:31
                    ثُمَّ ٱلْجَحِيمَ صَلُّوهُ
                
                
                
                
                
                    69:31
                    "Sa'an nan, a cikin Jahĩm, ku ƙõna shi."  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:32
                    ثُمَّ فِى سِلْسِلَةٍ ذَرْعُهَا سَبْعُونَ ذِرَاعًا فَٱسْلُكُوهُ
                
                
                
                
                
                    69:32
                    "Sa'an nan, acikin sarƙa, tsawonta zirã'i saba'in, sai ku sanya shi."  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:33
                    إِنَّهُۥ كَانَ لَا يُؤْمِنُ بِٱللَّهِ ٱلْعَظِيمِ
                
                
                
                
                
                    69:33
                    "Lalle ne, shi ya kasance ba ya yin ĩmãni da Allah, Mai girma!"  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:34
                    وَلَا يَحُضُّ عَلَىٰ طَعَامِ ٱلْمِسْكِينِ
                
                
                
                
                
                    69:34
                    "Kuma ba ya kwaɗaitarwa ga (bãyar da) abincin matalauci!"  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:35
                    فَلَيْسَ لَهُ ٱلْيَوْمَ هَـٰهُنَا حَمِيمٌ
                
                
                
                
                
                    69:35
                    "Sabõda haka, a yau, a nan, bã ya da masõyi."  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:36
                    وَلَا طَعَامٌ إِلَّا مِنْ غِسْلِينٍ
                
                
                
                
                
                    69:36
                    "Kuma bãbu wani abinci, sai daga (itãcen) gislĩn."  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:37
                    لَّا يَأْكُلُهُۥٓ إِلَّا ٱلْخَـٰطِـُٔونَ
                
                
                
                
                
                    69:37
                    "Bãbu mai cin sa sai mãsu ganganci."  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:38
                    فَلَآ أُقْسِمُ بِمَا تُبْصِرُونَ
                
                
                
                
                
                    69:38
                    To, ba sai Nã yi rantsuwa da abin da kuke iya gani ba,  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:39
                    وَمَا لَا تُبْصِرُونَ
                
                
                
                
                
                    69:39
                    Da abin da bã ku iya gani.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:40
                    إِنَّهُۥ لَقَوْلُ رَسُولٍ كَرِيمٍ
                
                
                
                
                
                    69:40
                    Lalle ne, shi (Alƙur'ani) tabbas maganar wani manzo (Jibirilu) mai daraja ne.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:41
                    وَمَا هُوَ بِقَوْلِ شَاعِرٍ ۚ قَلِيلًا مَّا تُؤْمِنُونَ
                
                
                
                
                
                    69:41
                    Kuma shi ba maganar wani mawãƙi ba ne. Kaɗan ƙwarai zã ku gaskata.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:42
                    وَلَا بِقَوْلِ كَاهِنٍ ۚ قَلِيلًا مَّا تَذَكَّرُونَ
                
                
                
                
                
                    69:42
                    Kuma bã maganar bõka ba ne. Kaɗan ƙwarai zã ku iya tunãwa.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:43
                    تَنزِيلٌ مِّن رَّبِّ ٱلْعَـٰلَمِينَ
                
                
                
                
                
                    69:43
                    Abin saukarwã ne daga Ubangijin halitta duka.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:44
                    وَلَوْ تَقَوَّلَ عَلَيْنَا بَعْضَ ٱلْأَقَاوِيلِ
                
                
                
                
                
                    69:44
                    Kuma dã (Muhammadu) yã faɗi wata maganã, yã jingina ta garẽ Mu.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:45
                    لَأَخَذْنَا مِنْهُ بِٱلْيَمِينِ
                
                
                
                
                
                    69:45
                    Dã Mun kãma shi da dãma.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:46
                    ثُمَّ لَقَطَعْنَا مِنْهُ ٱلْوَتِينَ
                
                
                
                
                
                    69:46
                    sa'an nan, lalle ne, dã Mun kãtse masa lakã.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:47
                    فَمَا مِنكُم مِّنْ أَحَدٍ عَنْهُ حَـٰجِزِينَ
                
                
                
                
                
                    69:47
                    Kuma daga cikinku bãbu wasu mãsu iya kãre (azãbarMu) daga gare shi.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:48
                    وَإِنَّهُۥ لَتَذْكِرَةٌ لِّلْمُتَّقِينَ
                
                
                
                
                
                    69:48
                    Kuma lalle ne shi (Alƙur'ãni) tanãtarwa ce ga mãsu taƙawa.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:49
                    وَإِنَّا لَنَعْلَمُ أَنَّ مِنكُم مُّكَذِّبِينَ
                
                
                
                
                
                    69:49
                    Kuma lalle, ne Mũ, wallahi Munã sane da cẽwa daga cikinku alwwai mãsu ƙaryatãwa.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:50
                    وَإِنَّهُۥ لَحَسْرَةٌ عَلَى ٱلْكَـٰفِرِينَ
                
                
                
                
                
                    69:50
                    Kuma lalle ne shi (Alƙarãni) wallahi baƙin ciki ne ga kãfirai.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:51
                    وَإِنَّهُۥ لَحَقُّ ٱلْيَقِينِ
                
                
                
                
                
                    69:51
                    Kuma lalle, ne shi gaskiya ce ta yaƙshẽni.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    69:52
                    فَسَبِّحْ بِٱسْمِ رَبِّكَ ٱلْعَظِيمِ
                
                
                
                
                
                    69:52
                    Sabõda haka, ka tsarkake sũnan Ubangjinka, mai girma.  - Abubakar Gumi (Hausa)