Selected

Original Text
Abubakar Gumi

Available Translations

26 Ash-Shu`arā' ٱلشُّعَرَاء

< Previous   227 Āyah   The Poets      Next >  

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.

26:1 طسٓمٓ
26:1
Abubakar Gumi (Hausa) :
¦. S̃. M̃.

26:2 تِلْكَ ءَايَـٰتُ ٱلْكِتَـٰبِ ٱلْمُبِينِ
26:2
Abubakar Gumi (Hausa) :
Waɗancan ãyõyin Littãfi ne bayyananne.

26:3 لَعَلَّكَ بَـٰخِعٌ نَّفْسَكَ أَلَّا يَكُونُوا۟ مُؤْمِنِينَ
26:3
Abubakar Gumi (Hausa) :
Tsammãninka kai mai halakar da ranka ne, dõmin ba su kasance mũminai ba!

26:4 إِن نَّشَأْ نُنَزِّلْ عَلَيْهِم مِّنَ ٱلسَّمَآءِ ءَايَةً فَظَلَّتْ أَعْنَـٰقُهُمْ لَهَا خَـٰضِعِينَ
26:4
Abubakar Gumi (Hausa) :
Idan Mun so zã Mu saukar, a kansu, da wata ãyã daga sama, sai wuyõyinsu su yini sabõda ita sunã mãsu ƙasƙantar da kai.

26:5 وَمَا يَأْتِيهِم مِّن ذِكْرٍ مِّنَ ٱلرَّحْمَـٰنِ مُحْدَثٍ إِلَّا كَانُوا۟ عَنْهُ مُعْرِضِينَ
26:5
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma wata tunãtarwa ba ta jẽ musu ba, daga Mai rahama, sãbuwa, fãce sun kasance daga barinta sunã mãsu bijirẽwa.

26:6 فَقَدْ كَذَّبُوا۟ فَسَيَأْتِيهِمْ أَنۢبَـٰٓؤُا۟ مَا كَانُوا۟ بِهِۦ يَسْتَهْزِءُونَ
26:6
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, lalle ne, sun ƙaryata, to, lãbãran abin da suka kasance sunã yi na izgili da shi zã ya je musu.

26:7 أَوَلَمْ يَرَوْا۟ إِلَى ٱلْأَرْضِ كَمْ أَنۢبَتْنَا فِيهَا مِن كُلِّ زَوْجٍ كَرِيمٍ
26:7
Abubakar Gumi (Hausa) :
Shin, ba su dũba ba zuwa ga ƙasa, da yawa Muka tsirar a cikinta, daga dukan nau'i mai kyau?

26:8 إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَـَٔايَةً ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ
26:8
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne, a cikin wancan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mũminai ba.

26:9 وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلْعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ
26:9
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai rahama.

26:10 وَإِذْ نَادَىٰ رَبُّكَ مُوسَىٰٓ أَنِ ٱئْتِ ٱلْقَوْمَ ٱلظَّـٰلِمِينَ
26:10
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma a lõkacin da Ubangijinka Ya kirãyi Mũsã, "Ka je wa mutãnen nan azzãlumai.

26:11 قَوْمَ فِرْعَوْنَ ۚ أَلَا يَتَّقُونَ
26:11
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Mutãnen Fir'auna bã zã su yi taƙawa ba?"

26:12 قَالَ رَبِّ إِنِّىٓ أَخَافُ أَن يُكَذِّبُونِ
26:12
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ya ce: "Ya Ubangijĩna, nĩ inã tsõron su ƙaryata ni.

26:13 وَيَضِيقُ صَدْرِى وَلَا يَنطَلِقُ لِسَانِى فَأَرْسِلْ إِلَىٰ هَـٰرُونَ
26:13
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma ƙirjĩna ya yi ƙunci kuma harshẽna bã zai saku ba sabõda haka ka aika zuwa ga Harũna.

26:14 وَلَهُمْ عَلَىَّ ذَنۢبٌ فَأَخَافُ أَن يَقْتُلُونِ
26:14
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma sunã da wani laifi a kaina, sabõda haka inã tsõron kada su kashe ni."

26:15 قَالَ كَلَّا ۖ فَٱذْهَبَا بِـَٔايَـٰتِنَآ ۖ إِنَّا مَعَكُم مُّسْتَمِعُونَ
26:15
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ya ce: "Kayya! Ku tafi, kũ biyu, da ÃyõyinMu. Lalle ne, Munã tãre da ku Munã Mãsu saurãre."

26:16 فَأْتِيَا فِرْعَوْنَ فَقُولَآ إِنَّا رَسُولُ رَبِّ ٱلْعَـٰلَمِينَ
26:16
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Sai ku je wa Fir'auna, sa'an nan ku ce, Lalle ne, mu, Manzannin Ubangijin halitta ne."

26:17 أَنْ أَرْسِلْ مَعَنَا بَنِىٓ إِسْرَٰٓءِيلَ
26:17
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Ka saki Banĩ Isrã'ila tãre da mu."

26:18 قَالَ أَلَمْ نُرَبِّكَ فِينَا وَلِيدًا وَلَبِثْتَ فِينَا مِنْ عُمُرِكَ سِنِينَ
26:18
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ya ce: "Shin, ba mu yi rẽnonka ba a cikinmu kanã jãrĩri, kuma ka zauna a cikinmu shẽkarudaga lõkacin rãyuwarka?"

26:19 وَفَعَلْتَ فَعْلَتَكَ ٱلَّتِى فَعَلْتَ وَأَنتَ مِنَ ٱلْكَـٰفِرِينَ
26:19
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma ka aikata aikinka wanda ka aikata alhãli kai kanã daga butulai?"

26:20 قَالَ فَعَلْتُهَآ إِذًا وَأَنَا۠ مِنَ ٱلضَّآلِّينَ
26:20
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ya ce: "Na aikata shi a lõkacin inã daga mãsu jãhilcin hushi."

26:21 فَفَرَرْتُ مِنكُمْ لَمَّا خِفْتُكُمْ فَوَهَبَ لِى رَبِّى حُكْمًا وَجَعَلَنِى مِنَ ٱلْمُرْسَلِينَ
26:21
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Sabõda haka na gudu daga gãre ku a lõkacin da na ji tsõronku, sai Ubangijĩna Ya bã ni hukunci, kuma Ya sanya ni daga Manzanni."

26:22 وَتِلْكَ نِعْمَةٌ تَمُنُّهَا عَلَىَّ أَنْ عَبَّدتَّ بَنِىٓ إِسْرَٰٓءِيلَ
26:22
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma waccan ni'ima ce, kanã gõrint a kaina, dõmin kã bautar da Banĩ Isrã'ĩla."

26:23 قَالَ فِرْعَوْنُ وَمَا رَبُّ ٱلْعَـٰلَمِينَ
26:23
Abubakar Gumi (Hausa) :
Fir'auna ya ce: "Kuma mene ne Ubangijin halittu?"

26:24 قَالَ رَبُّ ٱلسَّمَـٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ وَمَا بَيْنَهُمَآ ۖ إِن كُنتُم مُّوقِنِينَ
26:24
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ya ce: "Ubangijin sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu, idan kun kasance mãsu ƙarfin ĩmãni."

26:25 قَالَ لِمَنْ حَوْلَهُۥٓ أَلَا تَسْتَمِعُونَ
26:25
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ya ce wa waɗanda suke a gẽfensa, "Bã za ku saurãra ba?"

26:26 قَالَ رَبُّكُمْ وَرَبُّ ءَابَآئِكُمُ ٱلْأَوَّلِينَ
26:26
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ya ce: "Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku na farko."

26:27 قَالَ إِنَّ رَسُولَكُمُ ٱلَّذِىٓ أُرْسِلَ إِلَيْكُمْ لَمَجْنُونٌ
26:27
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ya ce: "Lalle ne Manzonku, wanda aka aiko zuwa gare ku, haƙi ƙa, mahaukaci ne."

26:28 قَالَ رَبُّ ٱلْمَشْرِقِ وَٱلْمَغْرِبِ وَمَا بَيْنَهُمَآ ۖ إِن كُنتُمْ تَعْقِلُونَ
26:28
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ya ce: "Ubangijin mafitar rãnã da maɓũyarta da abin dayake a tsakaninsu, idan kun kasance kunã hankalta."

26:29 قَالَ لَئِنِ ٱتَّخَذْتَ إِلَـٰهًا غَيْرِى لَأَجْعَلَنَّكَ مِنَ ٱلْمَسْجُونِينَ
26:29
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ya ce: "Lalle ne idan ka riƙi wani abin bautãwa wanĩna haƙĩƙa, inã sanyã ka daga ɗaurarru."

26:30 قَالَ أَوَلَوْ جِئْتُكَ بِشَىْءٍ مُّبِينٍ
26:30
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ya ce: "Ashe, kuma kõ dã nã zõ maka da wani, abu mai bayyanãwa?"

26:31 قَالَ فَأْتِ بِهِۦٓ إِن كُنتَ مِنَ ٱلصَّـٰدِقِينَ
26:31
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ya ce: "To, ka zõ da shi idan ka kasance daga, mãsu gaskiya."

26:32 فَأَلْقَىٰ عَصَاهُ فَإِذَا هِىَ ثُعْبَانٌ مُّبِينٌ
26:32
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai ya jẽfa sandarsa, sai ga ta kumurci bayyananne.

26:33 وَنَزَعَ يَدَهُۥ فَإِذَا هِىَ بَيْضَآءُ لِلنَّـٰظِرِينَ
26:33
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma ya fizge hannunsa, sai ga shi fari ga mãsu kallo.

26:34 قَالَ لِلْمَلَإِ حَوْلَهُۥٓ إِنَّ هَـٰذَا لَسَـٰحِرٌ عَلِيمٌ
26:34
Abubakar Gumi (Hausa) :
(Fir'auna) ya ce ga mashãwarta a gẽfensa, "Lalle ne, wannan haƙĩƙa, masihirci ne, mai ilmi!

26:35 يُرِيدُ أَن يُخْرِجَكُم مِّنْ أَرْضِكُم بِسِحْرِهِۦ فَمَاذَا تَأْمُرُونَ
26:35
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Yanã son ya fitar da ku daga ƙasarku game da sihirinSa. To mẽne ne kuke shãwartãwa?"

26:36 قَالُوٓا۟ أَرْجِهْ وَأَخَاهُ وَٱبْعَثْ فِى ٱلْمَدَآئِنِ حَـٰشِرِينَ
26:36
Abubakar Gumi (Hausa) :
Suka ce: "Ka jinkirtar da shi, shĩ da ɗan'uwansa, kuma ka aika mãsu gayya a cikin birãne."

26:37 يَأْتُوكَ بِكُلِّ سَحَّارٍ عَلِيمٍ
26:37
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Zã su zõ maka da dukkan mai yawan sihiri masani."

26:38 فَجُمِعَ ٱلسَّحَرَةُ لِمِيقَـٰتِ يَوْمٍ مَّعْلُومٍ
26:38
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai aka tãra masihirta dõmin ajalin yini sananne.

26:39 وَقِيلَ لِلنَّاسِ هَلْ أَنتُم مُّجْتَمِعُونَ
26:39
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma aka ce wa mutãne "Kõ kũ mãsu tãruwã ne?

26:40 لَعَلَّنَا نَتَّبِعُ ٱلسَّحَرَةَ إِن كَانُوا۟ هُمُ ٱلْغَـٰلِبِينَ
26:40
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Tsammãninmu mu bi masihirta, idan sun kasance sũ ne marinjãya."

26:41 فَلَمَّا جَآءَ ٱلسَّحَرَةُ قَالُوا۟ لِفِرْعَوْنَ أَئِنَّ لَنَا لَأَجْرًا إِن كُنَّا نَحْنُ ٱلْغَـٰلِبِينَ
26:41
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, a lõkacin da masihirta suka jẽ suka ce wa Fir'auna,"Shin, lalle ne, haƙĩƙa munã da ijãra idan mun kasance mũ ne marinjãya?"

26:42 قَالَ نَعَمْ وَإِنَّكُمْ إِذًا لَّمِنَ ٱلْمُقَرَّبِينَ
26:42
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ya ce: "Na'am! Kuma lalle ne, kũ ne a lõkacin haƙĩƙa muƙarrabai."

26:43 قَالَ لَهُم مُّوسَىٰٓ أَلْقُوا۟ مَآ أَنتُم مُّلْقُونَ
26:43
Abubakar Gumi (Hausa) :
Mũsã ya ce musu, "Ku jẽfa abin da kuke mãsu jẽfãwa."

26:44 فَأَلْقَوْا۟ حِبَالَهُمْ وَعِصِيَّهُمْ وَقَالُوا۟ بِعِزَّةِ فِرْعَوْنَ إِنَّا لَنَحْنُ ٱلْغَـٰلِبُونَ
26:44
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai suka jẽfa igiyõyinsu, da sandunansu, kuma suka ce: "Da ƙarfin Fir'auna lalle ne mũ, haƙĩƙa, mũ ne marinjãya."

26:45 فَأَلْقَىٰ مُوسَىٰ عَصَاهُ فَإِذَا هِىَ تَلْقَفُ مَا يَأْفِكُونَ
26:45
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai Mũsa ya jẽfa sandarsa, sai ga ta tanã harhaɗe abin da suke yi na ƙarya.

26:46 فَأُلْقِىَ ٱلسَّحَرَةُ سَـٰجِدِينَ
26:46
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai aka jẽfar da masihirta sunã mãsu sujada.

26:47 قَالُوٓا۟ ءَامَنَّا بِرَبِّ ٱلْعَـٰلَمِينَ
26:47
Abubakar Gumi (Hausa) :
Suka ce: "Mun yi ĩmãni da Ubangijin halitta."

26:48 رَبِّ مُوسَىٰ وَهَـٰرُونَ
26:48
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Ubangijin Mũsa da Hãrũna."

26:49 قَالَ ءَامَنتُمْ لَهُۥ قَبْلَ أَنْ ءَاذَنَ لَكُمْ ۖ إِنَّهُۥ لَكَبِيرُكُمُ ٱلَّذِى عَلَّمَكُمُ ٱلسِّحْرَ فَلَسَوْفَ تَعْلَمُونَ ۚ لَأُقَطِّعَنَّ أَيْدِيَكُمْ وَأَرْجُلَكُم مِّنْ خِلَـٰفٍ وَلَأُصَلِّبَنَّكُمْ أَجْمَعِينَ
26:49
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ya ce: "Ashe, kun yi ĩmãni sabõda shĩ, a gabãnin in yi muku izni? Lalle ne shi, haƙĩƙa babbanku ne wanda ya kõya muku sihirin, to, zã ku sani. Lalle ne haƙĩƙa, zan kakkãtse hannuwanku da kafãfunku a tarnaƙi, kuma haƙĩƙa, zan tsĩrẽ ku gabã ɗaya."

26:50 قَالُوا۟ لَا ضَيْرَ ۖ إِنَّآ إِلَىٰ رَبِّنَا مُنقَلِبُونَ
26:50
Abubakar Gumi (Hausa) :
Suka ce: "Bãbu wata cũta! Lalle ne mũ mãsu jũyãwa ne zuwa ga Ubangijinmu."

26:51 إِنَّا نَطْمَعُ أَن يَغْفِرَ لَنَا رَبُّنَا خَطَـٰيَـٰنَآ أَن كُنَّآ أَوَّلَ ٱلْمُؤْمِنِينَ
26:51
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Lalle ne mu munã kwaɗayin Ubangijinmu, Ya gãfarta mana kurakuranmu dõmin mun kasance farkon mãsu ĩmãni."

26:52 ۞ وَأَوْحَيْنَآ إِلَىٰ مُوسَىٰٓ أَنْ أَسْرِ بِعِبَادِىٓ إِنَّكُم مُّتَّبَعُونَ
26:52
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma Muka aika zuwa ga Mũsã cẽwa ka yi tafiyar dare da bãyiNa, lalle ne kũ waɗanda ake biyã ne.

26:53 فَأَرْسَلَ فِرْعَوْنُ فِى ٱلْمَدَآئِنِ حَـٰشِرِينَ
26:53
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai Fir'auna ya aika mãsu gayya a cikin birãne.

26:54 إِنَّ هَـٰٓؤُلَآءِ لَشِرْذِمَةٌ قَلِيلُونَ
26:54
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Lalle ne, waɗannan, haƙĩƙa, ƙungiya ce kaɗan."

26:55 وَإِنَّهُمْ لَنَا لَغَآئِظُونَ
26:55
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma lalle ne sũ, a gare Mu, Mãsu fusãtarwa ne."

26:56 وَإِنَّا لَجَمِيعٌ حَـٰذِرُونَ
26:56
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma lalle ne mũ haƙĩƙa gabã ɗaya mãsu sauna ne."

26:57 فَأَخْرَجْنَـٰهُم مِّن جَنَّـٰتٍ وَعُيُونٍ
26:57
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai Muka fitar da su daga gonaki da marẽmari.

26:58 وَكُنُوزٍ وَمَقَامٍ كَرِيمٍ
26:58
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da taskõki da mazauni mai kyau.

26:59 كَذَٰلِكَ وَأَوْرَثْنَـٰهَا بَنِىٓ إِسْرَٰٓءِيلَ
26:59
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kamar haka! Kuma Muka gãdar da su ga Banĩ Isrãĩla.

26:60 فَأَتْبَعُوهُم مُّشْرِقِينَ
26:60
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai suka bĩ su sunã mãsu fita a lõkacin hũdõwar rãnã.

26:61 فَلَمَّا تَرَٰٓءَا ٱلْجَمْعَانِ قَالَ أَصْحَـٰبُ مُوسَىٰٓ إِنَّا لَمُدْرَكُونَ
26:61
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan a lõkacin da jama'a biyu suka ga jũna, sai abõkan Mũsã suka ce: "Lalle ne mũ haƙĩ ƙa, waɗanda ake riska ne."

26:62 قَالَ كَلَّآ ۖ إِنَّ مَعِىَ رَبِّى سَيَهْدِينِ
26:62
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ya ce: "Kayya! Lalle ne Ubangijina Yanã tare da ni, zai shiryar da ni."

26:63 فَأَوْحَيْنَآ إِلَىٰ مُوسَىٰٓ أَنِ ٱضْرِب بِّعَصَاكَ ٱلْبَحْرَ ۖ فَٱنفَلَقَ فَكَانَ كُلُّ فِرْقٍ كَٱلطَّوْدِ ٱلْعَظِيمِ
26:63
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai Muka yi wahayi zuwa ga Mũsã cẽwa "Ka dõki tẽku da sandarka." Sai tẽku ta tsãge, kõwane tsãgi ya kasance kamar falalen dũtse mai girma.

26:64 وَأَزْلَفْنَا ثَمَّ ٱلْـَٔاخَرِينَ
26:64
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma Muka kusantar da waɗansu mutãne a can.

26:65 وَأَنجَيْنَا مُوسَىٰ وَمَن مَّعَهُۥٓ أَجْمَعِينَ
26:65
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma Muka tsĩrar da Mũsã da waɗanda suke tãre da shi gabã ɗaya.

26:66 ثُمَّ أَغْرَقْنَا ٱلْـَٔاخَرِينَ
26:66
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan kuma Muka nutsar da waɗansu mutãnen.

26:67 إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَـَٔايَةً ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ
26:67
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba.

26:68 وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلْعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ
26:68
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma lalle ne Ubangijinka, kaƙĩƙa, Shĩ ne Mabũwayi, Mai jin ƙai.

26:69 وَٱتْلُ عَلَيْهِمْ نَبَأَ إِبْرَٰهِيمَ
26:69
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma ka karanta, a kansu, lãbãrin Ibrãhĩm.

26:70 إِذْ قَالَ لِأَبِيهِ وَقَوْمِهِۦ مَا تَعْبُدُونَ
26:70
Abubakar Gumi (Hausa) :
A sã'ilin da ya ce wa ubansa da mutãnensa, "Mẽne ne kuke bauta wa?"

26:71 قَالُوا۟ نَعْبُدُ أَصْنَامًا فَنَظَلُّ لَهَا عَـٰكِفِينَ
26:71
Abubakar Gumi (Hausa) :
Suka ce: "Munã bauta wa gumãka, sabõda haka munã yini mãsu lazimta a gare su."

26:72 قَالَ هَلْ يَسْمَعُونَكُمْ إِذْ تَدْعُونَ
26:72
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ya ce: "Shin, sunã jin ku, a lõkacin da kuke kira?"

26:73 أَوْ يَنفَعُونَكُمْ أَوْ يَضُرُّونَ
26:73
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kõ kuwa sunã amfãnin ku, kõ sunã cũtar ku?"

26:74 قَالُوا۟ بَلْ وَجَدْنَآ ءَابَآءَنَا كَذَٰلِكَ يَفْعَلُونَ
26:74
Abubakar Gumi (Hausa) :
Suka ce: "Ã'a mun sãmĩ ubanninmu, kamar haka ne suke aikatãwa."

26:75 قَالَ أَفَرَءَيْتُم مَّا كُنتُمْ تَعْبُدُونَ
26:75
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ya ce: "Shin to, kun ga abin da kuka kasance kunã bautã wa?"

26:76 أَنتُمْ وَءَابَآؤُكُمُ ٱلْأَقْدَمُونَ
26:76
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kũ da ubanninku mafi daɗẽwa?"

26:77 فَإِنَّهُمْ عَدُوٌّ لِّىٓ إِلَّا رَبَّ ٱلْعَـٰلَمِينَ
26:77
Abubakar Gumi (Hausa) :
"To lalle ne, sũ maƙiya ne a gare ni, fãce Ubangijin halittu."

26:78 ٱلَّذِى خَلَقَنِى فَهُوَ يَهْدِينِ
26:78
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Wanda Ya halitta ni, sa'an nan Yanã shiryar da ni."

26:79 وَٱلَّذِى هُوَ يُطْعِمُنِى وَيَسْقِينِ
26:79
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma Wanda Yake Shĩ ne Yake ciyar da ni, kuma Yanã shãyar da ni."

26:80 وَإِذَا مَرِضْتُ فَهُوَ يَشْفِينِ
26:80
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma idan na yi jiyya, to, Shĩ ne Yake warkar da ni."

26:81 وَٱلَّذِى يُمِيتُنِى ثُمَّ يُحْيِينِ
26:81
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma wanda Yake matar da ni, sa'an nan Ya rãyar da ni."

26:82 وَٱلَّذِىٓ أَطْمَعُ أَن يَغْفِرَ لِى خَطِيٓـَٔتِى يَوْمَ ٱلدِّينِ
26:82
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma wanda Yake inã kwaɗayin Ya gãfarta mini kurãkuraina, a rãnar sãkamako."

26:83 رَبِّ هَبْ لِى حُكْمًا وَأَلْحِقْنِى بِٱلصَّـٰلِحِينَ
26:83
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Ya Ubangijĩna! Ka ba ni hukunci, kuma Ka riskar da ni ga sãlihai."

26:84 وَٱجْعَل لِّى لِسَانَ صِدْقٍ فِى ٱلْـَٔاخِرِينَ
26:84
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma Ka sanya mini harshen gaskiya a cikin mutãnen ƙarshe."

26:85 وَٱجْعَلْنِى مِن وَرَثَةِ جَنَّةِ ٱلنَّعِيمِ
26:85
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma Ka sanya ni daga magãdan Aljannar ni'ima."

26:86 وَٱغْفِرْ لِأَبِىٓ إِنَّهُۥ كَانَ مِنَ ٱلضَّآلِّينَ
26:86
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma Ka gãfarta wa ubãna, lalle ne shi, ya kasance daga ɓatattu."

26:87 وَلَا تُخْزِنِى يَوْمَ يُبْعَثُونَ
26:87
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma kada Ka kunyata ni a rãnar da ake tãyar da su."

26:88 يَوْمَ لَا يَنفَعُ مَالٌ وَلَا بَنُونَ
26:88
Abubakar Gumi (Hausa) :
"A rãnar da dũkiya bã ta amfãni, kuma ɗiya bã su yi."

26:89 إِلَّا مَنْ أَتَى ٱللَّهَ بِقَلْبٍ سَلِيمٍ
26:89
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Fãce wanda ya jẽ wa Allah da zũciya mai tsarki."

26:90 وَأُزْلِفَتِ ٱلْجَنَّةُ لِلْمُتَّقِينَ
26:90
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma aka kusantar da Aljanna ga mãsu taƙawa.

26:91 وَبُرِّزَتِ ٱلْجَحِيمُ لِلْغَاوِينَ
26:91
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma aka fitar da wutã babba dõmin halakakku.

26:92 وَقِيلَ لَهُمْ أَيْنَ مَا كُنتُمْ تَعْبُدُونَ
26:92
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma aka ce musu, "Inã abin da kuka kasance kunã bautawa?"

26:93 مِن دُونِ ٱللَّهِ هَلْ يَنصُرُونَكُمْ أَوْ يَنتَصِرُونَ
26:93
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Baicin Allah? Shin sunã tamakon ku kõ kuwa sunã tsare kansu?"

26:94 فَكُبْكِبُوا۟ فِيهَا هُمْ وَٱلْغَاوُۥنَ
26:94
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai aka kikkife su a cikinta, su da halakakkun.

26:95 وَجُنُودُ إِبْلِيسَ أَجْمَعُونَ
26:95
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da rundunar Ibilĩsa gabã ɗaya.

26:96 قَالُوا۟ وَهُمْ فِيهَا يَخْتَصِمُونَ
26:96
Abubakar Gumi (Hausa) :
Suka ce: alhãli sunã a cikinta sunã yin husũma,

26:97 تَٱللَّهِ إِن كُنَّا لَفِى ضَلَـٰلٍ مُّبِينٍ
26:97
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Rantsuwa da Allah! Lalle ne mun kasance, haƙĩƙa, a cikin ɓata bayyananna."

26:98 إِذْ نُسَوِّيكُم بِرَبِّ ٱلْعَـٰلَمِينَ
26:98
Abubakar Gumi (Hausa) :
"A lõkacin da muke daidaita ku da Ubangijin halittu.

26:99 وَمَآ أَضَلَّنَآ إِلَّا ٱلْمُجْرِمُونَ
26:99
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma bãbu abin da ya ɓatar da mu fãce mãsu laifi."

26:100 فَمَا لَنَا مِن شَـٰفِعِينَ
26:100
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Sabõda haka bã mu da waɗansu macẽta."

26:101 وَلَا صَدِيقٍ حَمِيمٍ
26:101
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma bã mu da abõki, masõyi."

26:102 فَلَوْ أَنَّ لَنَا كَرَّةً فَنَكُونَ مِنَ ٱلْمُؤْمِنِينَ
26:102
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Sabõda haka dã lalle munã da (dãmar) kõmawa, dõmin mu kasance daga mũminai!"

26:103 إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَـَٔايَةً ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ
26:103
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne, a cikin wancan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, bã su kasance mũminai ba.

26:104 وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلْعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ
26:104
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma lalle ne, Ubangijinka, Shi ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.

26:105 كَذَّبَتْ قَوْمُ نُوحٍ ٱلْمُرْسَلِينَ
26:105
Abubakar Gumi (Hausa) :
Mutãnen Nũhu sun ƙaryata Manzanni.

26:106 إِذْ قَالَ لَهُمْ أَخُوهُمْ نُوحٌ أَلَا تَتَّقُونَ
26:106
Abubakar Gumi (Hausa) :
A lõkacin da ɗan'uwansu, Nũhu, ya ce musu, "Shin, bã zã ku yi taƙawa ba?"

26:107 إِنِّى لَكُمْ رَسُولٌ أَمِينٌ
26:107
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Lalle ne, zuwa gare ku, ni Manzo ne amintacce."

26:108 فَٱتَّقُوا۟ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ
26:108
Abubakar Gumi (Hausa) :
"To, ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."

26:109 وَمَآ أَسْـَٔلُكُمْ عَلَيْهِ مِنْ أَجْرٍ ۖ إِنْ أَجْرِىَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ ٱلْعَـٰلَمِينَ
26:109
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma bã ni tambayar ku wata ijãra a kansa. Ijãrãtã ba ta zama ba fãce daga Ubangijin halittu."

26:110 فَٱتَّقُوا۟ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ
26:110
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Sabõda haka, ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."

26:111 ۞ قَالُوٓا۟ أَنُؤْمِنُ لَكَ وَٱتَّبَعَكَ ٱلْأَرْذَلُونَ
26:111
Abubakar Gumi (Hausa) :
Suka ce: "Ashe, zã mu yi ĩmãni sabõda kai alhãli kuwa mafiya ƙasƙanci sun bi ka?"

26:112 قَالَ وَمَا عِلْمِى بِمَا كَانُوا۟ يَعْمَلُونَ
26:112
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ya ce: "Kuma bã ni da sani ga abin da suka kasance sanã aikatãwa."

26:113 إِنْ حِسَابُهُمْ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّى ۖ لَوْ تَشْعُرُونَ
26:113
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Hisãbinsu bai zama ba fãce ga Ubangijina, dã kunã sansancẽwa."

26:114 وَمَآ أَنَا۠ بِطَارِدِ ٱلْمُؤْمِنِينَ
26:114
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Ban zama mai kõre mũminai ba."

26:115 إِنْ أَنَا۠ إِلَّا نَذِيرٌ مُّبِينٌ
26:115
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Nĩ ba kõwa ba ne sai mai gargaɗi mai bayyanãwa."

26:116 قَالُوا۟ لَئِن لَّمْ تَنتَهِ يَـٰنُوحُ لَتَكُونَنَّ مِنَ ٱلْمَرْجُومِينَ
26:116
Abubakar Gumi (Hausa) :
Suka ce: "Lalle ne, idan ba ka hanu ba, yã Nũhu, (daga maganarka,) haƙĩƙa, kanã kasancẽwa daga waɗanda ake jẽfewa"

26:117 قَالَ رَبِّ إِنَّ قَوْمِى كَذَّبُونِ
26:117
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ya ce: "Yã Ubangijĩna! Lalle ne mutãnena sun ƙaryatã ni."

26:118 فَٱفْتَحْ بَيْنِى وَبَيْنَهُمْ فَتْحًا وَنَجِّنِى وَمَن مَّعِىَ مِنَ ٱلْمُؤْمِنِينَ
26:118
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Sai ka yi hukunci, a tsakãnĩna da tsakãninsu tabbataccen hukanci, kuma ka tsĩrar da ni, da waɗanda suke tãre da ni daga mũminai."

26:119 فَأَنجَيْنَـٰهُ وَمَن مَّعَهُۥ فِى ٱلْفُلْكِ ٱلْمَشْحُونِ
26:119
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai Muka tsĩrar da shi, shi da waɗanda suke tãre da shi, a cikin jirgi wanda aka yi wa lõdi.

26:120 ثُمَّ أَغْرَقْنَا بَعْدُ ٱلْبَاقِينَ
26:120
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan Muka nutsar a bãyan haka, da sauran.

26:121 إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَـَٔايَةً ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ
26:121
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, ba su kasance mãsu ĩmãni ba.

26:122 وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلْعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ
26:122
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma Lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai Rahama.

26:123 كَذَّبَتْ عَادٌ ٱلْمُرْسَلِينَ
26:123
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ãdãwa sun ƙaryata Manzanni.

26:124 إِذْ قَالَ لَهُمْ أَخُوهُمْ هُودٌ أَلَا تَتَّقُونَ
26:124
Abubakar Gumi (Hausa) :
A lõkacin da ɗan'uwansu, Hũdu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"

26:125 إِنِّى لَكُمْ رَسُولٌ أَمِينٌ
26:125
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Lalle ne ni, zuwa gare ku, haƙĩƙa, Manzo ne, amintacce."

26:126 فَٱتَّقُوا۟ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ
26:126
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."

26:127 وَمَآ أَسْـَٔلُكُمْ عَلَيْهِ مِنْ أَجْرٍ ۖ إِنْ أَجْرِىَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ ٱلْعَـٰلَمِينَ
26:127
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma bã ni tambayar wata ijãra a kansa. Ijãrãta ba ta zama ba, fãce daga Ubangijin halittu."

26:128 أَتَبْنُونَ بِكُلِّ رِيعٍ ءَايَةً تَعْبَثُونَ
26:128
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Shin, kunã yin ginin sitadiyo a kõwane tsauni ne, kunã yin wãsa?"

26:129 وَتَتَّخِذُونَ مَصَانِعَ لَعَلَّكُمْ تَخْلُدُونَ
26:129
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma kunã riƙon matsãrar ruwa, tsammãninku, ku dawwama?"

26:130 وَإِذَا بَطَشْتُم بَطَشْتُمْ جَبَّارِينَ
26:130
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma idan kun yi damƙa, sai ku yi damƙar kunã mãsu tanƙwasãwa."

26:131 فَٱتَّقُوا۟ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ
26:131
Abubakar Gumi (Hausa) :
"To ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."

26:132 وَٱتَّقُوا۟ ٱلَّذِىٓ أَمَدَّكُم بِمَا تَعْلَمُونَ
26:132
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Ku ji tsõron wanda Ya taimake ku da abin da kuka sani."

26:133 أَمَدَّكُم بِأَنْعَـٰمٍ وَبَنِينَ
26:133
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Ya taimake ku da dabbõbin ni'ima da ɗiya."

26:134 وَجَنَّـٰتٍ وَعُيُونٍ
26:134
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Da gõnaki da marẽmari."

26:135 إِنِّىٓ أَخَافُ عَلَيْكُمْ عَذَابَ يَوْمٍ عَظِيمٍ
26:135
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Lalle ne nĩ, inã ji muku tsõron azãbar wani yini mai girma."

26:136 قَالُوا۟ سَوَآءٌ عَلَيْنَآ أَوَعَظْتَ أَمْ لَمْ تَكُن مِّنَ ٱلْوَٰعِظِينَ
26:136
Abubakar Gumi (Hausa) :
Suka ce: "Daidai ne a kanmu: Kã yi wa'azi kõ ba ka kasance daga mãsu wa'azi ba."

26:137 إِنْ هَـٰذَآ إِلَّا خُلُقُ ٱلْأَوَّلِينَ
26:137
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Wannan abu bai zamõ ba fãce hãlãyen mutãnen farko."

26:138 وَمَا نَحْنُ بِمُعَذَّبِينَ
26:138
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma mũ ba mu zama waɗanda ake yi wa azãba ba."

26:139 فَكَذَّبُوهُ فَأَهْلَكْنَـٰهُمْ ۗ إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَـَٔايَةً ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ
26:139
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sabõda haka suka ƙaryata shi, sai Muka halakar da sũ. Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba.

26:140 وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلْعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ
26:140
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shi ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.

26:141 كَذَّبَتْ ثَمُودُ ٱلْمُرْسَلِينَ
26:141
Abubakar Gumi (Hausa) :
Samũdãwa sun ƙaryata Manzanni.

26:142 إِذْ قَالَ لَهُمْ أَخُوهُمْ صَـٰلِحٌ أَلَا تَتَّقُونَ
26:142
Abubakar Gumi (Hausa) :
A lõkacin da ɗan'uwansu Sãlihu ya ce: "Shin, bã zã ku bi Allah da taƙawa ba?"

26:143 إِنِّى لَكُمْ رَسُولٌ أَمِينٌ
26:143
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Lalle ne nĩ zuwã gare ku, Manzo ne, amintacce."

26:144 فَٱتَّقُوا۟ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ
26:144
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã.

26:145 وَمَآ أَسْـَٔلُكُمْ عَلَيْهِ مِنْ أَجْرٍ ۖ إِنْ أَجْرِىَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ ٱلْعَـٰلَمِينَ
26:145
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma bã ni tambayar ku wata ijãra a kansa. Ijãrãta ba ta zama ba fãce da a Ubangijin halittu."

26:146 أَتُتْرَكُونَ فِى مَا هَـٰهُنَآ ءَامِنِينَ
26:146
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Shin, anã barin ku a cikin abin da yake a nan, kunã amintattu?"

26:147 فِى جَنَّـٰتٍ وَعُيُونٍ
26:147
Abubakar Gumi (Hausa) :
"A cikin gõnaki da marẽmari."

26:148 وَزُرُوعٍ وَنَخْلٍ طَلْعُهَا هَضِيمٌ
26:148
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Da shuke-shuke da dabĩ nai, 'ya'yan itãcensu hirtsi mãsu narkẽwa a ciki?"

26:149 وَتَنْحِتُونَ مِنَ ٱلْجِبَالِ بُيُوتًا فَـٰرِهِينَ
26:149
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma kunã sassaƙa gidãje daga duwãtsu, kunã mãsu alfãhari?"

26:150 فَٱتَّقُوا۟ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ
26:150
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."

26:151 وَلَا تُطِيعُوٓا۟ أَمْرَ ٱلْمُسْرِفِينَ
26:151
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kada ku yi ɗã'ã ga umurnin maɓarnata."

26:152 ٱلَّذِينَ يُفْسِدُونَ فِى ٱلْأَرْضِ وَلَا يُصْلِحُونَ
26:152
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Waɗanda suke yin ɓarna a cikin ƙasa, kuma bã su kyautatãwa."

26:153 قَالُوٓا۟ إِنَّمَآ أَنتَ مِنَ ٱلْمُسَحَّرِينَ
26:153
Abubakar Gumi (Hausa) :
Suka ce: "Kai daga mãsu sihiri kurum kake."

26:154 مَآ أَنتَ إِلَّا بَشَرٌ مِّثْلُنَا فَأْتِ بِـَٔايَةٍ إِن كُنتَ مِنَ ٱلصَّـٰدِقِينَ
26:154
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Bã kõwa kake ba, fãce mutum kamarmu. To, kã zo da wata ãyã idan kã kasance daga mãsu gaskiya."

26:155 قَالَ هَـٰذِهِۦ نَاقَةٌ لَّهَا شِرْبٌ وَلَكُمْ شِرْبُ يَوْمٍ مَّعْلُومٍ
26:155
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ya ce: "Wannan rãkuma ce tanã da shan yini, kuma kunã da shan yini sasanne."

26:156 وَلَا تَمَسُّوهَا بِسُوٓءٍ فَيَأْخُذَكُمْ عَذَابُ يَوْمٍ عَظِيمٍ
26:156
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kada ku shãfe ta da cũta har azãbar yini mai girmã ta shãfe ku."

26:157 فَعَقَرُوهَا فَأَصْبَحُوا۟ نَـٰدِمِينَ
26:157
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai suka sõke ta sa'an nan suka wãyi gari sunã mãsu nadãma.

26:158 فَأَخَذَهُمُ ٱلْعَذَابُ ۗ إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَـَٔايَةً ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ
26:158
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sabõda haka azãba ta kãma su. Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, ba su kasance mãsu ĩmãni ba.

26:159 وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلْعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ
26:159
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne Ubangijinka, haƙĩ ƙa, Shĩ ne Mabuwayi, Mai jin ƙai.

26:160 كَذَّبَتْ قَوْمُ لُوطٍ ٱلْمُرْسَلِينَ
26:160
Abubakar Gumi (Hausa) :
Mutãnen Lũɗu sun ƙaryata Manzanni.

26:161 إِذْ قَالَ لَهُمْ أَخُوهُمْ لُوطٌ أَلَا تَتَّقُونَ
26:161
Abubakar Gumi (Hausa) :
A lõkacin da ɗan'uwansu, Lũɗu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"

26:162 إِنِّى لَكُمْ رَسُولٌ أَمِينٌ
26:162
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Lalle ne nĩ, zuwa gare ku, Manzõ ne, amintacce."

26:163 فَٱتَّقُوا۟ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ
26:163
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."

26:164 وَمَآ أَسْـَٔلُكُمْ عَلَيْهِ مِنْ أَجْرٍ ۖ إِنْ أَجْرِىَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ ٱلْعَـٰلَمِينَ
26:164
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma bã ni tambayar ku wata ijãra, Ijãrãta ba ta zama ba fãce daga Ubangijin halittu."

26:165 أَتَأْتُونَ ٱلذُّكْرَانَ مِنَ ٱلْعَـٰلَمِينَ
26:165
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Shin kunã jẽ wa maza daga cikin talikai?"

26:166 وَتَذَرُونَ مَا خَلَقَ لَكُمْ رَبُّكُم مِّنْ أَزْوَٰجِكُم ۚ بَلْ أَنتُمْ قَوْمٌ عَادُونَ
26:166
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma kunã barin abin da Ubangijinku Ya halitta muku daga mãtanku? Ã'a, ku mutãne ne mãsu ƙẽtarẽwa!"

26:167 قَالُوا۟ لَئِن لَّمْ تَنتَهِ يَـٰلُوطُ لَتَكُونَنَّ مِنَ ٱلْمُخْرَجِينَ
26:167
Abubakar Gumi (Hausa) :
Suka ce: "Lalle ne haƙĩƙa idan ba ka hanu ba, yã Lũɗu! Tĩlas ne kanã kasancẽwa daga waɗanda ake fitarwa (daga gari)."

26:168 قَالَ إِنِّى لِعَمَلِكُم مِّنَ ٱلْقَالِينَ
26:168
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ya ce: "Lalle ne ga aikinku, haƙĩƙa, inã daga mãsu ƙinsa."

26:169 رَبِّ نَجِّنِى وَأَهْلِى مِمَّا يَعْمَلُونَ
26:169
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Ya Ubangijina! Ka tsĩrar da ni da iyãlĩna daga abin da suke aikatãwa."

26:170 فَنَجَّيْنَـٰهُ وَأَهْلَهُۥٓ أَجْمَعِينَ
26:170
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sabõda haka Muka tsĩrar da shi, Shi da mutãnensa gabã ɗaya.

26:171 إِلَّا عَجُوزًا فِى ٱلْغَـٰبِرِينَ
26:171
Abubakar Gumi (Hausa) :
Fãce wata tsõhuwa a cikin mãsu wanzuwa.

26:172 ثُمَّ دَمَّرْنَا ٱلْـَٔاخَرِينَ
26:172
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan kuma Muka darkãke wasu.

26:173 وَأَمْطَرْنَا عَلَيْهِم مَّطَرًا ۖ فَسَآءَ مَطَرُ ٱلْمُنذَرِينَ
26:173
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma Muka yi ruwan sama a kansu ruwa, sai dai ruwan waɗanda ake yi wa gargaɗi ya mũnana.

26:174 إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَـَٔايَةً ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ
26:174
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne ga wannan, akwai ãyã, kuma mafi yawansu bã su kasance mãsu ĩmãni ba.

26:175 وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلْعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ
26:175
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma lalle ne Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.

26:176 كَذَّبَ أَصْحَـٰبُ لْـَٔيْكَةِ ٱلْمُرْسَلِينَ
26:176
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ma'abũta ƙunci sun ƙaryata Manzanni.

26:177 إِذْ قَالَ لَهُمْ شُعَيْبٌ أَلَا تَتَّقُونَ
26:177
Abubakar Gumi (Hausa) :
A lõkacin da Shu'aibu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"

26:178 إِنِّى لَكُمْ رَسُولٌ أَمِينٌ
26:178
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Lalle ne ni, zuwa gare ku, Manzo ne, amintacce."

26:179 فَٱتَّقُوا۟ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ
26:179
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa kuma ku yi mini ɗã'ã."

26:180 وَمَآ أَسْـَٔلُكُمْ عَلَيْهِ مِنْ أَجْرٍ ۖ إِنْ أَجْرِىَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ ٱلْعَـٰلَمِينَ
26:180
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma ba ni tambayar ku wata ijãra a kansa. Ijãrata ba ta zama ba fãce daga Ubangijin halittu."

26:181 ۞ أَوْفُوا۟ ٱلْكَيْلَ وَلَا تَكُونُوا۟ مِنَ ٱلْمُخْسِرِينَ
26:181
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Ku cika mũdu, kuma kada ku kasance daga mãsu sanyãwar hasãra (ga mutãne)."

26:182 وَزِنُوا۟ بِٱلْقِسْطَاسِ ٱلْمُسْتَقِيمِ
26:182
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma ku yi awo da sikẽli daidaitacce."

26:183 وَلَا تَبْخَسُوا۟ ٱلنَّاسَ أَشْيَآءَهُمْ وَلَا تَعْثَوْا۟ فِى ٱلْأَرْضِ مُفْسِدِينَ
26:183
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma kada ku nakasa wa mutãne abũbuwansu kuma kada ku yi fasãdi a cikin ƙasa kuna mãsu ɓarna."

26:184 وَٱتَّقُوا۟ ٱلَّذِى خَلَقَكُمْ وَٱلْجِبِلَّةَ ٱلْأَوَّلِينَ
26:184
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma ku ji tsõron Allah wanda Ya halitta ku, kũ da jama'ar farko."

26:185 قَالُوٓا۟ إِنَّمَآ أَنتَ مِنَ ٱلْمُسَحَّرِينَ
26:185
Abubakar Gumi (Hausa) :
Suka ce: "Kai dai daga waɗanda suke sihirtattu kawai ne."

26:186 وَمَآ أَنتَ إِلَّا بَشَرٌ مِّثْلُنَا وَإِن نَّظُنُّكَ لَمِنَ ٱلْكَـٰذِبِينَ
26:186
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma bã kõwa kake ba, fãce mutum kamarmu kuma lalle ne munã zaton ka, haƙĩƙa, daga maƙaryata."

26:187 فَأَسْقِطْ عَلَيْنَا كِسَفًا مِّنَ ٱلسَّمَآءِ إِن كُنتَ مِنَ ٱلصَّـٰدِقِينَ
26:187
Abubakar Gumi (Hausa) :
"To ka jẽfo wani ɓaɓɓake daga sama a kanmu, idan ka kasance daga mãsu gaskiya."

26:188 قَالَ رَبِّىٓ أَعْلَمُ بِمَا تَعْمَلُونَ
26:188
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ya ce: "Ubangijĩna ne Mafi sani ga abin da kuke aikatãwa."

26:189 فَكَذَّبُوهُ فَأَخَذَهُمْ عَذَابُ يَوْمِ ٱلظُّلَّةِ ۚ إِنَّهُۥ كَانَ عَذَابَ يَوْمٍ عَظِيمٍ
26:189
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai suka ƙaiyatã shi, sabõda haka, azãbar rãnar girgije ta kãma su. Lalle ne ita, tã kasance azãbar yini mai girma.

26:190 إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَـَٔايَةً ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ
26:190
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle a cikin wancan haƙĩka akwai ãya, amma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba.

26:191 وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلْعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ
26:191
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma lalle Ubangijĩnka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.

26:192 وَإِنَّهُۥ لَتَنزِيلُ رَبِّ ٱلْعَـٰلَمِينَ
26:192
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma lalle shi (Alƙur'ãni), haƙĩƙa, saukarwar Ubangijinhalittu ne.

26:193 نَزَلَ بِهِ ٱلرُّوحُ ٱلْأَمِينُ
26:193
Abubakar Gumi (Hausa) :
Rũhi amintacce ne ya sauka da shi.

26:194 عَلَىٰ قَلْبِكَ لِتَكُونَ مِنَ ٱلْمُنذِرِينَ
26:194
Abubakar Gumi (Hausa) :
A kan zũciyarka, dõmin ka kasance daga mãsu gargaɗi.

26:195 بِلِسَانٍ عَرَبِىٍّ مُّبِينٍ
26:195
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da harshe na Larabci mai bayãni.

26:196 وَإِنَّهُۥ لَفِى زُبُرِ ٱلْأَوَّلِينَ
26:196
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma lalle shin, haƙĩƙa, yanã a cikin litattafan (Manzannin) farko.

26:197 أَوَلَمْ يَكُن لَّهُمْ ءَايَةً أَن يَعْلَمَهُۥ عُلَمَـٰٓؤُا۟ بَنِىٓ إِسْرَٰٓءِيلَ
26:197
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ashe, bai kasance ãyã ba a gare su, ya zama Mãlaman Banĩ Isrã'ĩla sun san shi?

26:198 وَلَوْ نَزَّلْنَـٰهُ عَلَىٰ بَعْضِ ٱلْأَعْجَمِينَ
26:198
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma dã mun saukar da shi a kan sãshen Ajamãwa,

26:199 فَقَرَأَهُۥ عَلَيْهِم مَّا كَانُوا۟ بِهِۦ مُؤْمِنِينَ
26:199
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ya karanta shi a kansu, ba su kasance sabõda shi mãsu ĩmãni ba.

26:200 كَذَٰلِكَ سَلَكْنَـٰهُ فِى قُلُوبِ ٱلْمُجْرِمِينَ
26:200
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kamar wancan ne! Muka shigar da shi a cikin zukãtan mãsu laifi.

26:201 لَا يُؤْمِنُونَ بِهِۦ حَتَّىٰ يَرَوُا۟ ٱلْعَذَابَ ٱلْأَلِيمَ
26:201
Abubakar Gumi (Hausa) :
Bã zã su yi ĩmãni da shĩ ba sai sun ga azãbar nan mai raɗadi.

26:202 فَيَأْتِيَهُم بَغْتَةً وَهُمْ لَا يَشْعُرُونَ
26:202
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai ta taho musu kwatsam, alhãli kuwa sũ, ba su sansance ba.

26:203 فَيَقُولُوا۟ هَلْ نَحْنُ مُنظَرُونَ
26:203
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai su ce: "Shin, mu waɗanda ake yi wa jinkiri ne?"

26:204 أَفَبِعَذَابِنَا يَسْتَعْجِلُونَ
26:204
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ashe, to, da azãbarMu suke nẽman gaggãwa?

26:205 أَفَرَءَيْتَ إِن مَّتَّعْنَـٰهُمْ سِنِينَ
26:205
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ashe, to, kã gani, idan Muka jĩshe su daɗi a shẽkaru,

26:206 ثُمَّ جَآءَهُم مَّا كَانُوا۟ يُوعَدُونَ
26:206
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan abin da suka kasance anã yi musu wa'adi (da shi) ya jẽ musu,

26:207 مَآ أَغْنَىٰ عَنْهُم مَّا كَانُوا۟ يُمَتَّعُونَ
26:207
Abubakar Gumi (Hausa) :
Abin da suka kasance anã jĩshe su dãɗin bã zai tunkuɗe azãba ba daga gare su.

26:208 وَمَآ أَهْلَكْنَا مِن قَرْيَةٍ إِلَّا لَهَا مُنذِرُونَ
26:208
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma bã Mu halakar da wata alƙarya ba fãce tanã da mãsu gargaɗi.

26:209 ذِكْرَىٰ وَمَا كُنَّا ظَـٰلِمِينَ
26:209
Abubakar Gumi (Hausa) :
Dõmin tunãtarwa, kuma ba Mu kasance Mãsu zãlunci ba.

26:210 وَمَا تَنَزَّلَتْ بِهِ ٱلشَّيَـٰطِينُ
26:210
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma (Alƙur'ãni) Shaiɗãnu ba su ɗõra sauka da shĩba.

26:211 وَمَا يَنۢبَغِى لَهُمْ وَمَا يَسْتَطِيعُونَ
26:211
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma bã ya kamãta a gare su (su Shaiɗãnu su sauka da shi), kuma ba su iyãwa.

26:212 إِنَّهُمْ عَنِ ٱلسَّمْعِ لَمَعْزُولُونَ
26:212
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne sũ, daga saurãre, haƙĩƙa, waɗanda aka nĩsantar ne.

26:213 فَلَا تَدْعُ مَعَ ٱللَّهِ إِلَـٰهًا ءَاخَرَ فَتَكُونَ مِنَ ٱلْمُعَذَّبِينَ
26:213
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sabõda haka, kada ka kira wani abin bautãwa na dabam tãre da Allah, sai ka kasance daga waɗanda ake yi wa azãba.

26:214 وَأَنذِرْ عَشِيرَتَكَ ٱلْأَقْرَبِينَ
26:214
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma ka yi gargaɗi ga danginka mafiya kusanci.

26:215 وَٱخْفِضْ جَنَاحَكَ لِمَنِ ٱتَّبَعَكَ مِنَ ٱلْمُؤْمِنِينَ
26:215
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma ka sassauta fikãfikanka ga wanda ya bĩ ka daga mũminai.

26:216 فَإِنْ عَصَوْكَ فَقُلْ إِنِّى بَرِىٓءٌ مِّمَّا تَعْمَلُونَ
26:216
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan idan suka sãɓã maka to ka ce: "Lalle nĩ, barrantacce ne daga abin da kuko aikatãwa."

26:217 وَتَوَكَّلْ عَلَى ٱلْعَزِيزِ ٱلرَّحِيمِ
26:217
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma ka dõgara ga Mabuwãyi, Mai jin ƙai.

26:218 ٱلَّذِى يَرَىٰكَ حِينَ تَقُومُ
26:218
Abubakar Gumi (Hausa) :
Wanda Yake ganin ka a lõkacin da kake tãshi tsaye.

26:219 وَتَقَلُّبَكَ فِى ٱلسَّـٰجِدِينَ
26:219
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da jujjuyãwarka a cikin mãsu yin sujada.

26:220 إِنَّهُۥ هُوَ ٱلسَّمِيعُ ٱلْعَلِيمُ
26:220
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle Shi, Shi ne Mai ji, Masani.

26:221 هَلْ أُنَبِّئُكُمْ عَلَىٰ مَن تَنَزَّلُ ٱلشَّيَـٰطِينُ
26:221
Abubakar Gumi (Hausa) :
Shin, (kunã so) in gaya muku a kan wanda Shaiɗãnnu kan sauka?

26:222 تَنَزَّلُ عَلَىٰ كُلِّ أَفَّاكٍ أَثِيمٍ
26:222
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sukan sauka a kan dukkan maƙaryaci, mai zunubi.

26:223 يُلْقُونَ ٱلسَّمْعَ وَأَكْثَرُهُمْ كَـٰذِبُونَ
26:223
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sunã jẽfa (abin da suka) ji, alhãli kuwa mafi yawansu maƙaryata ne.

26:224 وَٱلشُّعَرَآءُ يَتَّبِعُهُمُ ٱلْغَاوُۥنَ
26:224
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma mawãƙa halakakku ne ke bin su.

26:225 أَلَمْ تَرَ أَنَّهُمْ فِى كُلِّ وَادٍ يَهِيمُونَ
26:225
Abubakar Gumi (Hausa) :
Shin, ba ku cẽwa, lalle ne sũ, cikin kõwane rango sunã yin ɗimuwa (su ƙẽtare haddi) ba?

26:226 وَأَنَّهُمْ يَقُولُونَ مَا لَا يَفْعَلُونَ
26:226
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma lalle ne, sũ, sunã faɗin abin da bã su aikatãwa?

26:227 إِلَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ وَعَمِلُوا۟ ٱلصَّـٰلِحَـٰتِ وَذَكَرُوا۟ ٱللَّهَ كَثِيرًا وَٱنتَصَرُوا۟ مِنۢ بَعْدِ مَا ظُلِمُوا۟ ۗ وَسَيَعْلَمُ ٱلَّذِينَ ظَلَمُوٓا۟ أَىَّ مُنقَلَبٍ يَنقَلِبُونَ
26:227
Abubakar Gumi (Hausa) :
Fãce waɗanda suka yi ĩmãni suka aikata ayyukan ƙwarai, kuma suka ambaci Allah da yawa, kuma suka rãma zãlunci, daga bãyan an zãlunce su. Kuma waɗanda suka yi zãlunci, zã su sani a wace majũya suke jũyãwa.