Selected
Original Text
Abubakar Gumi
Abdullah Yusuf Ali
Abdul Majid Daryabadi
Abul Ala Maududi
Ahmed Ali
Ahmed Raza Khan
A. J. Arberry
Ali Quli Qarai
Hasan al-Fatih Qaribullah and Ahmad Darwish
Mohammad Habib Shakir
Mohammed Marmaduke William Pickthall
Muhammad Sarwar
Muhammad Taqi-ud-Din al-Hilali and Muhammad Muhsin Khan
Safi-ur-Rahman al-Mubarakpuri
Saheeh International
Talal Itani
Transliteration
Wahiduddin Khan
بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.
83:1
وَيْلٌ لِّلْمُطَفِّفِينَ
83:1
Bone ya tabbata ga mãsu naƙƙasãwa. - Abubakar Gumi (Hausa)
83:2
ٱلَّذِينَ إِذَا ٱكْتَالُوا۟ عَلَى ٱلنَّاسِ يَسْتَوْفُونَ
83:2
Waɗanda suke idan suka auna daga mutãne suna cika mũdu. - Abubakar Gumi (Hausa)
83:3
وَإِذَا كَالُوهُمْ أَو وَّزَنُوهُمْ يُخْسِرُونَ
83:3
Kuma idan sun auna musu da zakka ko da sikẽli, suna ragẽwa - Abubakar Gumi (Hausa)
83:4
أَلَا يَظُنُّ أُو۟لَـٰٓئِكَ أَنَّهُم مَّبْعُوثُونَ
83:4
Ashe! Waɗancan bã su tabbata cẽwa lalle sũ, ana tãyar da su ba? - Abubakar Gumi (Hausa)
83:5
لِيَوْمٍ عَظِيمٍ
83:5
Domin yini mai girma. - Abubakar Gumi (Hausa)
83:6
يَوْمَ يَقُومُ ٱلنَّاسُ لِرَبِّ ٱلْعَـٰلَمِينَ
83:6
Yinin da mutãne ke tãshi zuwa ga Ubangijin halitta? - Abubakar Gumi (Hausa)
83:7
كَلَّآ إِنَّ كِتَـٰبَ ٱلْفُجَّارِ لَفِى سِجِّينٍ
83:7
Haƙĩƙa lalle ne littãfin fãjirai dãhir, yana a cikin Sijjĩn. - Abubakar Gumi (Hausa)
83:8
وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا سِجِّينٌ
83:8
Kuma, mẽ ya sanar da kai abin da akẽ cẽ wa Sijjĩn? - Abubakar Gumi (Hausa)
83:9
كِتَـٰبٌ مَّرْقُومٌ
83:9
Wani 1ittãfi ne rubũtacce. - Abubakar Gumi (Hausa)
83:10
وَيْلٌ يَوْمَئِذٍ لِّلْمُكَذِّبِينَ
83:10
Bone yã tabbata a rãnar nan ga mãsu ƙaryatãwa. - Abubakar Gumi (Hausa)
83:11
ٱلَّذِينَ يُكَذِّبُونَ بِيَوْمِ ٱلدِّينِ
83:11
Waɗanda suke ƙaryatãwa game da rãnar sakamako. - Abubakar Gumi (Hausa)
83:12
وَمَا يُكَذِّبُ بِهِۦٓ إِلَّا كُلُّ مُعْتَدٍ أَثِيمٍ
83:12
Babũ mai ƙaryatãwa gare shi fãce dukan mai ƙẽtare haddi mai yawan zunubi. - Abubakar Gumi (Hausa)
83:13
إِذَا تُتْلَىٰ عَلَيْهِ ءَايَـٰتُنَا قَالَ أَسَـٰطِيرُ ٱلْأَوَّلِينَ
83:13
Idan ana karãtun ãyõyinmu, a kansa, sai ya ce: tãtsũniyõyin mutãnen farko ne. - Abubakar Gumi (Hausa)
83:14
كَلَّا ۖ بَلْ ۜ رَانَ عَلَىٰ قُلُوبِهِم مَّا كَانُوا۟ يَكْسِبُونَ
83:14
A'aha! Bã haka ba, abin da suka kasance suna aikatãwa dai, yã yi tsãtsa a cikin zukãtãnsu. - Abubakar Gumi (Hausa)
83:15
كَلَّآ إِنَّهُمْ عَن رَّبِّهِمْ يَوْمَئِذٍ لَّمَحْجُوبُونَ
83:15
A'aha! Haƙĩƙa, lalle ne sũ daga Ubangijinsu, rãnar nan, waɗanda ake shãmakancẽwa ne. - Abubakar Gumi (Hausa)
83:16
ثُمَّ إِنَّهُمْ لَصَالُوا۟ ٱلْجَحِيمِ
83:16
Sa'an nan, lalle ne, sũ mãsu shiga cikin Jahĩm ne. - Abubakar Gumi (Hausa)
83:17
ثُمَّ يُقَالُ هَـٰذَا ٱلَّذِى كُنتُم بِهِۦ تُكَذِّبُونَ
83:17
Sa'an nan a ce: "Wannan shi ne abin da kuka kasance kuna ƙaryatãwa game da shi." - Abubakar Gumi (Hausa)
83:18
كَلَّآ إِنَّ كِتَـٰبَ ٱلْأَبْرَارِ لَفِى عِلِّيِّينَ
83:18
A'aha! Haƙĩƙa lalle ne littãfin mãsu ɗã'ã yana a cikin Illiyyĩna? - Abubakar Gumi (Hausa)
83:19
وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا عِلِّيُّونَ
83:19
Kuma mẽne ne yã sanar da kai abin da ake cẽwa Illiyyũna? - Abubakar Gumi (Hausa)
83:20
كِتَـٰبٌ مَّرْقُومٌ
83:20
Wani littãfi ne rubũtacce. - Abubakar Gumi (Hausa)
83:21
يَشْهَدُهُ ٱلْمُقَرَّبُونَ
83:21
Muƙarrabai suke halarta shi. - Abubakar Gumi (Hausa)
83:22
إِنَّ ٱلْأَبْرَارَ لَفِى نَعِيمٍ
83:22
Lalle ne, mãsu ɗã'ã ga Allah tabbas suna cikin ni'ima. - Abubakar Gumi (Hausa)
83:23
عَلَى ٱلْأَرَآئِكِ يَنظُرُونَ
83:23
A kan karagu, suna ta kallo. - Abubakar Gumi (Hausa)
83:24
تَعْرِفُ فِى وُجُوهِهِمْ نَضْرَةَ ٱلنَّعِيمِ
83:24
Kana sani a cikin huskõkinsu, akwai kwarjinin ni'ima. - Abubakar Gumi (Hausa)
83:25
يُسْقَوْنَ مِن رَّحِيقٍ مَّخْتُومٍ
83:25
Ana shãyar da sũ daga wata giya wadda aka yunƙe a kan rufinta. - Abubakar Gumi (Hausa)
83:26
خِتَـٰمُهُۥ مِسْكٌ ۚ وَفِى ذَٰلِكَ فَلْيَتَنَافَسِ ٱلْمُتَنَـٰفِسُونَ
83:26
¡arshen kurɓinta miski ne. To, a cikin wannan, mãsu gwagwarmaya su yi ta gwagwarmayar nẽma. - Abubakar Gumi (Hausa)
83:27
وَمِزَاجُهُۥ مِن تَسْنِيمٍ
83:27
Kuma abin da ake gauraya ta da shi, daga tasnĩm yake. - Abubakar Gumi (Hausa)
83:28
عَيْنًا يَشْرَبُ بِهَا ٱلْمُقَرَّبُونَ
83:28
(Wato) wani marmaro ne wanda muƙarrabai ke sha daga gare shi. - Abubakar Gumi (Hausa)
83:29
إِنَّ ٱلَّذِينَ أَجْرَمُوا۟ كَانُوا۟ مِنَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ يَضْحَكُونَ
83:29
Lalle ne, waɗanda suka kãfirta sun kasance (a dũniya) suna yi wa waɗanda suka yi ĩmãni dãriya. - Abubakar Gumi (Hausa)
83:30
وَإِذَا مَرُّوا۟ بِهِمْ يَتَغَامَزُونَ
83:30
Kuma idan sun shuɗe su sai su dinga yin zunɗe. - Abubakar Gumi (Hausa)
83:31
وَإِذَا ٱنقَلَبُوٓا۟ إِلَىٰٓ أَهْلِهِمُ ٱنقَلَبُوا۟ فَكِهِينَ
83:31
Kuma idan suka jũya zuwa ga iyãlansu, sai su tafi suna kãkãci. - Abubakar Gumi (Hausa)
83:32
وَإِذَا رَأَوْهُمْ قَالُوٓا۟ إِنَّ هَـٰٓؤُلَآءِ لَضَآلُّونَ
83:32
Kuma idan sun gan su sai su ce: "Lalle waɗannan ɓatattu ne." - Abubakar Gumi (Hausa)
83:33
وَمَآ أُرْسِلُوا۟ عَلَيْهِمْ حَـٰفِظِينَ
83:33
Alhãli kuwa, ba a aike su ba dõmin su zama mãsu tsaro a kansu. - Abubakar Gumi (Hausa)
83:34
فَٱلْيَوْمَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ مِنَ ٱلْكُفَّارِ يَضْحَكُونَ
83:34
To, yau fa (a Lãhira] waɗanda suka yi ĩmãni, sũ ke yi wa kãfirai dãriya. - Abubakar Gumi (Hausa)
83:35
عَلَى ٱلْأَرَآئِكِ يَنظُرُونَ
83:35
A kan karagu, suna ta kallo. - Abubakar Gumi (Hausa)
83:36
هَلْ ثُوِّبَ ٱلْكُفَّارُ مَا كَانُوا۟ يَفْعَلُونَ
83:36
Shin an sãka ma kãfirai abin da suka kasance suna aikatawa? - Abubakar Gumi (Hausa)