Selected
Original Text
Abubakar Gumi
Abdullah Yusuf Ali
Abdul Majid Daryabadi
Abul Ala Maududi
Ahmed Ali
Ahmed Raza Khan
A. J. Arberry
Ali Quli Qarai
Hasan al-Fatih Qaribullah and Ahmad Darwish
Mohammad Habib Shakir
Mohammed Marmaduke William Pickthall
Muhammad Sarwar
Muhammad Taqi-ud-Din al-Hilali and Muhammad Muhsin Khan
Safi-ur-Rahman al-Mubarakpuri
Saheeh International
Talal Itani
Transliteration
Wahiduddin Khan
بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.
79:1
وَٱلنَّـٰزِعَـٰتِ غَرْقًا
79:1
Ina rantsuwa da mala'iku mãsu fisgar rãyuka (na kafirai) da ƙarfi. - Abubakar Gumi (Hausa)
79:2
وَٱلنَّـٰشِطَـٰتِ نَشْطًا
79:2
Da mãsu ɗibar rãyuka (na mũminai) da sauƙi a cikin nishãɗi. - Abubakar Gumi (Hausa)
79:3
وَٱلسَّـٰبِحَـٰتِ سَبْحًا
79:3
Da mãsu sauka daga sama da umurnin Allah kamar suna iyo. - Abubakar Gumi (Hausa)
79:4
فَٱلسَّـٰبِقَـٰتِ سَبْقًا
79:4
Sa'an nan, su zama mãsu gaugãwa (da umurnin Allah) kamar suna tsẽre. - Abubakar Gumi (Hausa)
79:5
فَٱلْمُدَبِّرَٰتِ أَمْرًا
79:5
Sa, an nan, su kasance masu shirya gudanar da umurni. - Abubakar Gumi (Hausa)
79:6
يَوْمَ تَرْجُفُ ٱلرَّاجِفَةُ
79:6
Rãnar da mai girgiza abũbuwa (bũsar farko) zã ta kaɗa. - Abubakar Gumi (Hausa)
79:7
تَتْبَعُهَا ٱلرَّادِفَةُ
79:7
Mai biyar ta (bũsa ta biyu) nã biye. - Abubakar Gumi (Hausa)
79:8
قُلُوبٌ يَوْمَئِذٍ وَاجِفَةٌ
79:8
Wasu zukãta, a rãnar nan, mãsu jin tsõro ne. - Abubakar Gumi (Hausa)
79:9
أَبْصَـٰرُهَا خَـٰشِعَةٌ
79:9
Alhãli idãnunsu na ƙasƙantattu. - Abubakar Gumi (Hausa)
79:10
يَقُولُونَ أَءِنَّا لَمَرْدُودُونَ فِى ٱلْحَافِرَةِ
79:10
Sunã cẽwa "Ashe lalle zã a iya mayar da mu a kan sãwunmu? - Abubakar Gumi (Hausa)
79:11
أَءِذَا كُنَّا عِظَـٰمًا نَّخِرَةً
79:11
"Ashe, idan muka zama ƙasusuwa rududdugaggu?" - Abubakar Gumi (Hausa)
79:12
قَالُوا۟ تِلْكَ إِذًا كَرَّةٌ خَاسِرَةٌ
79:12
Suka ce: "Waccan kam kõmãwa ce, tãɓaɓɓiya!" - Abubakar Gumi (Hausa)
79:13
فَإِنَّمَا هِىَ زَجْرَةٌ وَٰحِدَةٌ
79:13
To, ita kam, tsãwa guda kawai ce. - Abubakar Gumi (Hausa)
79:14
فَإِذَا هُم بِٱلسَّاهِرَةِ
79:14
Sai kawai gã su a bãyan ƙasa. - Abubakar Gumi (Hausa)
79:15
هَلْ أَتَىٰكَ حَدِيثُ مُوسَىٰٓ
79:15
Shin, lãbãrin Mũsã ya zo maka? - Abubakar Gumi (Hausa)
79:16
إِذْ نَادَىٰهُ رَبُّهُۥ بِٱلْوَادِ ٱلْمُقَدَّسِ طُوًى
79:16
A lõkacin da Ubangijinsa Ya kirãye shi, a cikin kwari mai tsarki, wato Duwã? - Abubakar Gumi (Hausa)
79:17
ٱذْهَبْ إِلَىٰ فِرْعَوْنَ إِنَّهُۥ طَغَىٰ
79:17
Ka tafi zuwa ga Fir'auna, lalle ne shi, ya ƙẽtare haddi. - Abubakar Gumi (Hausa)
79:18
فَقُلْ هَل لَّكَ إِلَىٰٓ أَن تَزَكَّىٰ
79:18
"Sai ka ce masa, Kõ zã ka so ka tsarkaka. - Abubakar Gumi (Hausa)
79:19
وَأَهْدِيَكَ إِلَىٰ رَبِّكَ فَتَخْشَىٰ
79:19
"Kuma in shiryar da kai zuwa ga Ubangijinka domin ka ji tsoronSa?" - Abubakar Gumi (Hausa)
79:20
فَأَرَىٰهُ ٱلْـَٔايَةَ ٱلْكُبْرَىٰ
79:20
Sai ya nũna masa ãyar nan mafi girma. - Abubakar Gumi (Hausa)
79:21
فَكَذَّبَ وَعَصَىٰ
79:21
Sai ya ƙaryata, kuma ya sãɓa (umurni), - Abubakar Gumi (Hausa)
79:22
ثُمَّ أَدْبَرَ يَسْعَىٰ
79:22
Sa'an nan ya jũya bãya, yanã tafiya da sauri. - Abubakar Gumi (Hausa)
79:23
فَحَشَرَ فَنَادَىٰ
79:23
Sai ya yi gayya, sa'an nan ya yi kira. - Abubakar Gumi (Hausa)
79:24
فَقَالَ أَنَا۠ رَبُّكُمُ ٱلْأَعْلَىٰ
79:24
Sai ya ce: "Nĩ ne Ubangijinku mafi ɗaudaka." - Abubakar Gumi (Hausa)
79:25
فَأَخَذَهُ ٱللَّهُ نَكَالَ ٱلْـَٔاخِرَةِ وَٱلْأُولَىٰٓ
79:25
Sabõda haka Allah Ya kama shi, dõmin azãbar maganar ƙarshe da ta farko. - Abubakar Gumi (Hausa)
79:26
إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَعِبْرَةً لِّمَن يَخْشَىٰٓ
79:26
Lalle ne, a cikin wannan haƙiƙa akwai abin kula ga wanda yake tsõron Allah. - Abubakar Gumi (Hausa)
79:27
ءَأَنتُمْ أَشَدُّ خَلْقًا أَمِ ٱلسَّمَآءُ ۚ بَنَىٰهَا
79:27
Shin, kũ ne mafi wuyar halitta ko sama? Allah Ya gina ta. - Abubakar Gumi (Hausa)
79:28
رَفَعَ سَمْكَهَا فَسَوَّىٰهَا
79:28
Ya ɗaukaka rufinta, sa'an nan Ya daidaita ta. - Abubakar Gumi (Hausa)
79:29
وَأَغْطَشَ لَيْلَهَا وَأَخْرَجَ ضُحَىٰهَا
79:29
Kuma Ya duhuntar da darenta, kuma Ya fitar da hantsinta. - Abubakar Gumi (Hausa)
79:30
وَٱلْأَرْضَ بَعْدَ ذَٰلِكَ دَحَىٰهَآ
79:30
Kuma, ƙasa a bayan haka Ya mulmula ta. - Abubakar Gumi (Hausa)
79:31
أَخْرَجَ مِنْهَا مَآءَهَا وَمَرْعَىٰهَا
79:31
Ya fitar da ruwanta daga gare ta da makiyãyarta. - Abubakar Gumi (Hausa)
79:32
وَٱلْجِبَالَ أَرْسَىٰهَا
79:32
Da duwatsu, Yã kafe ta. - Abubakar Gumi (Hausa)
79:33
مَتَـٰعًا لَّكُمْ وَلِأَنْعَـٰمِكُمْ
79:33
Domin jiyarwa dãɗi a gare ku, kuma ga dabbõbinku. - Abubakar Gumi (Hausa)
79:34
فَإِذَا جَآءَتِ ٱلطَّآمَّةُ ٱلْكُبْرَىٰ
79:34
To, idan uwar masĩfu, mafi girma, ta zo. - Abubakar Gumi (Hausa)
79:35
يَوْمَ يَتَذَكَّرُ ٱلْإِنسَـٰنُ مَا سَعَىٰ
79:35
Rãnar da mutum zai yi tunãnin abin da ya aikata. - Abubakar Gumi (Hausa)
79:36
وَبُرِّزَتِ ٱلْجَحِيمُ لِمَن يَرَىٰ
79:36
Kuma, a bayyana Jahĩm ga mai gani. - Abubakar Gumi (Hausa)
79:37
فَأَمَّا مَن طَغَىٰ
79:37
To, amma wanda ya yi girman kai. - Abubakar Gumi (Hausa)
79:38
وَءَاثَرَ ٱلْحَيَوٰةَ ٱلدُّنْيَا
79:38
Kuma, ya zãɓi rãyuwa ta kusa, (wato dũniya). - Abubakar Gumi (Hausa)
79:39
فَإِنَّ ٱلْجَحِيمَ هِىَ ٱلْمَأْوَىٰ
79:39
To, lalle ne Jahĩm, ita ce makõma. - Abubakar Gumi (Hausa)
79:40
وَأَمَّا مَنْ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِۦ وَنَهَى ٱلنَّفْسَ عَنِ ٱلْهَوَىٰ
79:40
Kuma, amma wanda ya ji tsõron tsayi a gaba ga Ubangijinsa, kuma ya kange kansa daga son rai. - Abubakar Gumi (Hausa)
79:41
فَإِنَّ ٱلْجَنَّةَ هِىَ ٱلْمَأْوَىٰ
79:41
To, lalle ne Aljanna ita ce makõma. - Abubakar Gumi (Hausa)
79:42
يَسْـَٔلُونَكَ عَنِ ٱلسَّاعَةِ أَيَّانَ مُرْسَىٰهَا
79:42
Sunã tambayar ka game da sa'a, wai yaushe ne matabbatarta? - Abubakar Gumi (Hausa)
79:43
فِيمَ أَنتَ مِن ذِكْرَىٰهَآ
79:43
Me ya haɗã ka da ambatonta? - Abubakar Gumi (Hausa)
79:44
إِلَىٰ رَبِّكَ مُنتَهَىٰهَآ
79:44
Zuwa ga Ubangijinka ƙarshen al'amarinta yake. - Abubakar Gumi (Hausa)
79:45
إِنَّمَآ أَنتَ مُنذِرُ مَن يَخْشَىٰهَا
79:45
Kai mai gargaɗi kawai ne ga mai tsõron ta. - Abubakar Gumi (Hausa)
79:46
كَأَنَّهُمْ يَوْمَ يَرَوْنَهَا لَمْ يَلْبَثُوٓا۟ إِلَّا عَشِيَّةً أَوْ ضُحَىٰهَا
79:46
Kamar sũ a rãnar da zã su gan ta, ba su zauna ba fãce a lõkacin marẽce ko hantsinsa. - Abubakar Gumi (Hausa)