Selected

Original Text
Abubakar Gumi

Available Translations

90 Al-Balad ٱلْبَلَد

< Previous   20 Āyah   The City      Next >  

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.

90:1 لَآ أُقْسِمُ بِهَـٰذَا ٱلْبَلَدِ
90:1
Abubakar Gumi (Hausa) :
Bã sai Na yi rantsuwa da wannan gari ba.

90:2 وَأَنتَ حِلٌّۢ بِهَـٰذَا ٱلْبَلَدِ
90:2
Abubakar Gumi (Hausa) :
Alhãli kai kanã mai sauka a cikin wannan gari.

90:3 وَوَالِدٍ وَمَا وَلَدَ
90:3
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da mahaifi da abin da ya haifa.

90:4 لَقَدْ خَلَقْنَا ٱلْإِنسَـٰنَ فِى كَبَدٍ
90:4
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne, Mun halitta mutum cikin wahala.

90:5 أَيَحْسَبُ أَن لَّن يَقْدِرَ عَلَيْهِ أَحَدٌ
90:5
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kõ yanã zaton bãbu wani mai iya sãmun iko, a kansa?

90:6 يَقُولُ أَهْلَكْتُ مَالًا لُّبَدًا
90:6
Abubakar Gumi (Hausa) :
Yana cẽwa "Na halakarda dũkiya mai yawa,"

90:7 أَيَحْسَبُ أَن لَّمْ يَرَهُۥٓ أَحَدٌ
90:7
Abubakar Gumi (Hausa) :
Shin, yana zaton cewa wani bai gan shi ba?

90:8 أَلَمْ نَجْعَل لَّهُۥ عَيْنَيْنِ
90:8
Abubakar Gumi (Hausa) :
Shin, ba Mu sanya masa idãnu biyu ba?

90:9 وَلِسَانًا وَشَفَتَيْنِ
90:9
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da harshe, da leɓɓa biyu.

90:10 وَهَدَيْنَـٰهُ ٱلنَّجْدَيْنِ
90:10
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma ba Mu shiryar da shi ga hanyõyi biyu ba?

90:11 فَلَا ٱقْتَحَمَ ٱلْعَقَبَةَ
90:11
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, don mene ne bai shiga Aƙabã ba?

90:12 وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا ٱلْعَقَبَةُ
90:12
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma mene ne ya sanar da kai abin da ake cẽ wa Aƙabã?

90:13 فَكُّ رَقَبَةٍ
90:13
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ita ce fansar wuyan bãwa.

90:14 أَوْ إِطْعَـٰمٌ فِى يَوْمٍ ذِى مَسْغَبَةٍ
90:14
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ko kuwa ciyarwa, a cikin yini ma'abũcin yunwa.

90:15 يَتِيمًا ذَا مَقْرَبَةٍ
90:15
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ga marãya ma'abũcin zumunta.

90:16 أَوْ مِسْكِينًا ذَا مَتْرَبَةٍ
90:16
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ko kuwa wani matalauci ma'abũcin turɓãya.

90:17 ثُمَّ كَانَ مِنَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ وَتَوَاصَوْا۟ بِٱلصَّبْرِ وَتَوَاصَوْا۟ بِٱلْمَرْحَمَةِ
90:17
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan kuma ya kasance daga waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka yi wa jũna wasiyya da yin haƙuri, kuma suka yi wa jũna wasiyya da tausayi.

90:18 أُو۟لَـٰٓئِكَ أَصْحَـٰبُ ٱلْمَيْمَنَةِ
90:18
Abubakar Gumi (Hausa) :
Waɗannan ne ma'abũta albarka

90:19 وَٱلَّذِينَ كَفَرُوا۟ بِـَٔايَـٰتِنَا هُمْ أَصْحَـٰبُ ٱلْمَشْـَٔمَةِ
90:19
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma waɗanda suka kãfirta da ãyõyinMu, sũ ne ma'abũta shu'umci

90:20 عَلَيْهِمْ نَارٌ مُّؤْصَدَةٌۢ
90:20
Abubakar Gumi (Hausa) :
A kansu akwai wata wuta abar kullewa.