Selected
Original Text
Abubakar Gumi
Abdullah Yusuf Ali
Abdul Majid Daryabadi
Abul Ala Maududi
Ahmed Ali
Ahmed Raza Khan
A. J. Arberry
Ali Quli Qarai
Hasan al-Fatih Qaribullah and Ahmad Darwish
Mohammad Habib Shakir
Mohammed Marmaduke William Pickthall
Muhammad Sarwar
Muhammad Taqi-ud-Din al-Hilali and Muhammad Muhsin Khan
Safi-ur-Rahman al-Mubarakpuri
Saheeh International
Talal Itani
Transliteration
Wahiduddin Khan
بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.
56:1
إِذَا وَقَعَتِ ٱلْوَاقِعَةُ
56:1
Idan mai aukuwa ta auku. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:2
لَيْسَ لِوَقْعَتِهَا كَاذِبَةٌ
56:2
Bãbu wani (rai) mai ƙaryatãwa ga aukuwarta. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:3
خَافِضَةٌ رَّافِعَةٌ
56:3
(Ita) mai ƙasƙantãwa ce, mai ɗaukakãwa. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:4
إِذَا رُجَّتِ ٱلْأَرْضُ رَجًّا
56:4
Idan aka girgiza ƙasã girgizwa. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:5
وَبُسَّتِ ٱلْجِبَالُ بَسًّا
56:5
Kuma aka niƙe duwãtsu, niƙẽwa. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:6
فَكَانَتْ هَبَآءً مُّنۢبَثًّا
56:6
Sai suka kasance ƙũra da ake wãtsarwa. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:7
وَكُنتُمْ أَزْوَٰجًا ثَلَـٰثَةً
56:7
Kuma kun kasance nau'i uku. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:8
فَأَصْحَـٰبُ ٱلْمَيْمَنَةِ مَآ أَصْحَـٰبُ ٱلْمَيْمَنَةِ
56:8
Watau mazõwa dãma. Mẽne ne mazõwa dãma? - Abubakar Gumi (Hausa)
56:9
وَأَصْحَـٰبُ ٱلْمَشْـَٔمَةِ مَآ أَصْحَـٰبُ ٱلْمَشْـَٔمَةِ
56:9
Da mazõwa hagu. Mẽne ne mazõwa hagu? - Abubakar Gumi (Hausa)
56:10
وَٱلسَّـٰبِقُونَ ٱلسَّـٰبِقُونَ
56:10
Da waɗanda suka tsẽre. Sũ wɗanda suka tsẽren nan, - Abubakar Gumi (Hausa)
56:11
أُو۟لَـٰٓئِكَ ٱلْمُقَرَّبُونَ
56:11
Waɗancan, sũ ne waɗanda aka kusantar. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:12
فِى جَنَّـٰتِ ٱلنَّعِيمِ
56:12
A ckin Aljannar ni'ima. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:13
ثُلَّةٌ مِّنَ ٱلْأَوَّلِينَ
56:13
Jama'a ne daga mutãnen farko. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:14
وَقَلِيلٌ مِّنَ ٱلْـَٔاخِرِينَ
56:14
Da kaɗan daga mutãnen ƙarshe. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:15
عَلَىٰ سُرُرٍ مَّوْضُونَةٍ
56:15
(Sunã) a kan wasu gadãje sãƙaƙƙuu. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:16
مُّتَّكِـِٔينَ عَلَيْهَا مُتَقَـٰبِلِينَ
56:16
Sunã gincire a kansu, sunã mãsu kallon jũna. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:17
يَطُوفُ عَلَيْهِمْ وِلْدَٰنٌ مُّخَلَّدُونَ
56:17
Wasu yara samãri na dindindin gẽwaya a kansu. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:18
بِأَكْوَابٍ وَأَبَارِيقَ وَكَأْسٍ مِّن مَّعِينٍ
56:18
Da wasu kõfuna da shantula da hinjãlai daga (giya) mai ɓuɓɓuga. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:19
لَّا يُصَدَّعُونَ عَنْهَا وَلَا يُنزِفُونَ
56:19
Bã a sanya musu cĩwon jirĩ sabõda ita, kuma bã su buguwa. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:20
وَفَـٰكِهَةٍ مِّمَّا يَتَخَيَّرُونَ
56:20
Da wasu 'ya'yan itãcen marmari daga irin waɗanda suke zãɓe. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:21
وَلَحْمِ طَيْرٍ مِّمَّا يَشْتَهُونَ
56:21
Da nãman tsuntsãye daga wanda suke ganin sha'awa. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:22
وَحُورٌ عِينٌ
56:22
Da wasu mãtã mãsu fararen idanu da girmansu. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:23
كَأَمْثَـٰلِ ٱللُّؤْلُؤِ ٱلْمَكْنُونِ
56:23
Kamar misãlan lu'ulu'u wanda aka ɓõye. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:24
جَزَآءًۢ بِمَا كَانُوا۟ يَعْمَلُونَ
56:24
A kan sakamakon, dõmin abin da suka kasance sunã aikatãwa. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:25
لَا يَسْمَعُونَ فِيهَا لَغْوًا وَلَا تَأْثِيمًا
56:25
Bã su jin wata yãsassar magana a cikinta, kuma bã su jin sun yi laifi. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:26
إِلَّا قِيلًا سَلَـٰمًا سَلَـٰمًا
56:26
Sai dai wata magana (mai dãɗi): Salãmun, Salãmun. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:27
وَأَصْحَـٰبُ ٱلْيَمِينِ مَآ أَصْحَـٰبُ ٱلْيَمِينِ
56:27
Da mazõwa dãma. Mẽne ne mazõwa dãma? - Abubakar Gumi (Hausa)
56:28
فِى سِدْرٍ مَّخْضُودٍ
56:28
(Sunã) a cikin itãcen magarya maras ƙaya. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:29
وَطَلْحٍ مَّنضُودٍ
56:29
Da wata ayaba mai yawan 'ya'ya. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:30
وَظِلٍّ مَّمْدُودٍ
56:30
Da wata inuwa mĩƙaƙƙiya. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:31
وَمَآءٍ مَّسْكُوبٍ
56:31
Da wani ruwa mai gudãna. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:32
وَفَـٰكِهَةٍ كَثِيرَةٍ
56:32
Da wasu 'ya'yan itacen marmari mãsu yawa. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:33
لَّا مَقْطُوعَةٍ وَلَا مَمْنُوعَةٍ
56:33
Bã su yankẽwa kuma bã a hana su. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:34
وَفُرُشٍ مَّرْفُوعَةٍ
56:34
Da wasu shimfiɗu maɗaukaka. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:35
إِنَّآ أَنشَأْنَـٰهُنَّ إِنشَآءً
56:35
Lalle Mũ, Mun ƙãga halittarsu ƙãgãwa. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:36
فَجَعَلْنَـٰهُنَّ أَبْكَارًا
56:36
Sa'an nan Muka sanya su budurwai. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:37
عُرُبًا أَتْرَابًا
56:37
Mãsu son mazansu, a cikin tsãrã ɗaya. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:38
لِّأَصْحَـٰبِ ٱلْيَمِينِ
56:38
Ga mazõwa dãma. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:39
ثُلَّةٌ مِّنَ ٱلْأَوَّلِينَ
56:39
Wata ƙungiya ce daga mutãnen farko. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:40
وَثُلَّةٌ مِّنَ ٱلْـَٔاخِرِينَ
56:40
Da wata ƙungiya daga mutãnen ƙarshe. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:41
وَأَصْحَـٰبُ ٱلشِّمَالِ مَآ أَصْحَـٰبُ ٱلشِّمَالِ
56:41
Mazõwa hagu, Mẽne ne mazõwa hagu? - Abubakar Gumi (Hausa)
56:42
فِى سَمُومٍ وَحَمِيمٍ
56:42
Sunã a cikin wata iskar zãfi da wani ruwan zãfi. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:43
وَظِلٍّ مِّن يَحْمُومٍ
56:43
Da wata inuwa ta hayãƙi mai baƙi. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:44
لَّا بَارِدٍ وَلَا كَرِيمٍ
56:44
Bã mai sanyi ba, kuma bã mai wata ni'ima ba. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:45
إِنَّهُمْ كَانُوا۟ قَبْلَ ذَٰلِكَ مُتْرَفِينَ
56:45
Lalle sũ, sun kasance a gabãnin wannan waɗanda aka jiyar dãɗi. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:46
وَكَانُوا۟ يُصِرُّونَ عَلَى ٱلْحِنثِ ٱلْعَظِيمِ
56:46
Kuma sun kasance sunã dõgẽwa a kan mummũnan zunubi mai girma. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:47
وَكَانُوا۟ يَقُولُونَ أَئِذَا مِتْنَا وَكُنَّا تُرَابًا وَعِظَـٰمًا أَءِنَّا لَمَبْعُوثُونَ
56:47
Kuma sun kasance sunã cẽwa: "Shin idan mun mutukuma muko kasance turɓãya da ƙasũsuwa shin lalle mũ waɗanda zã a kõma rãyarwa ne haƙĩƙatan?" - Abubakar Gumi (Hausa)
56:48
أَوَءَابَآؤُنَا ٱلْأَوَّلُونَ
56:48
"Shin, kuma da ubanninmu na farko?" - Abubakar Gumi (Hausa)
56:49
قُلْ إِنَّ ٱلْأَوَّلِينَ وَٱلْـَٔاخِرِينَ
56:49
Ka ce: "Lalle mutãnen farko da na ƙarshe." - Abubakar Gumi (Hausa)
56:50
لَمَجْمُوعُونَ إِلَىٰ مِيقَـٰتِ يَوْمٍ مَّعْلُومٍ
56:50
"Tabbas, waɗanda ake tãrãwa ne a cikin wani yini sananne." - Abubakar Gumi (Hausa)
56:51
ثُمَّ إِنَّكُمْ أَيُّهَا ٱلضَّآلُّونَ ٱلْمُكَذِّبُونَ
56:51
"Sa'an nan lalle ku, ya kũ ɓatattu, mãsu ƙaryatãwa!" - Abubakar Gumi (Hausa)
56:52
لَـَٔاكِلُونَ مِن شَجَرٍ مِّن زَقُّومٍ
56:52
"Lalle mãsu cĩ ne daga wata itãciya ta zaƙƙum (ɗanyen wutã)." - Abubakar Gumi (Hausa)
56:53
فَمَالِـُٔونَ مِنْهَا ٱلْبُطُونَ
56:53
"Har za ku zama mãsu cika cikunna daga gare ta." - Abubakar Gumi (Hausa)
56:54
فَشَـٰرِبُونَ عَلَيْهِ مِنَ ٱلْحَمِيمِ
56:54
"Sa'an nan kuma mãsu shã ne, a kan wannan abin cin, daga ruwan zãfi." - Abubakar Gumi (Hausa)
56:55
فَشَـٰرِبُونَ شُرْبَ ٱلْهِيمِ
56:55
"Ku zama mãsu shã irin shan rãƙuma mãsu ƙishirwa." - Abubakar Gumi (Hausa)
56:56
هَـٰذَا نُزُلُهُمْ يَوْمَ ٱلدِّينِ
56:56
Wannan ita ce liyãfarsu a rãnar sakamako. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:57
نَحْنُ خَلَقْنَـٰكُمْ فَلَوْلَا تُصَدِّقُونَ
56:57
Mũ ne Muka halitta ku, to, don me bã zã ku gaskata ba? - Abubakar Gumi (Hausa)
56:58
أَفَرَءَيْتُم مَّا تُمْنُونَ
56:58
Shin kuma kun ga abin da kuke fitarwa na maniyyi? - Abubakar Gumi (Hausa)
56:59
ءَأَنتُمْ تَخْلُقُونَهُۥٓ أَمْ نَحْنُ ٱلْخَـٰلِقُونَ
56:59
Shin kũ ne kuke halitta shi, kõ kuwa mũ ne Mãsu halittãwa? - Abubakar Gumi (Hausa)
56:60
نَحْنُ قَدَّرْنَا بَيْنَكُمُ ٱلْمَوْتَ وَمَا نَحْنُ بِمَسْبُوقِينَ
56:60
Mũ ne Muka ƙaddara mutuwa a tsakãninku, kuma ba Mu zama Mãsu gajiyãwa ba, - Abubakar Gumi (Hausa)
56:61
عَلَىٰٓ أَن نُّبَدِّلَ أَمْثَـٰلَكُمْ وَنُنشِئَكُمْ فِى مَا لَا تَعْلَمُونَ
56:61
A kan Mu musanya waɗansu (mutãne) kamarku, kuma Mu mayar da ku a cikin wata halitta da ba ku sani ba. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:62
وَلَقَدْ عَلِمْتُمُ ٱلنَّشْأَةَ ٱلْأُولَىٰ فَلَوْلَا تَذَكَّرُونَ
56:62
Kuma lalle, ne haƙĩƙa, kun san halittar farko, to, don me ba zã ku yi tunãni ba? - Abubakar Gumi (Hausa)
56:63
أَفَرَءَيْتُم مَّا تَحْرُثُونَ
56:63
Shin, kuma kun ga abin da kũke nõmãwa? - Abubakar Gumi (Hausa)
56:64
ءَأَنتُمْ تَزْرَعُونَهُۥٓ أَمْ نَحْنُ ٱلزَّٰرِعُونَ
56:64
Shin, kũ ne ke tsirar da shi kõ kuwa Mũ ne Mãsu tsirarwa? - Abubakar Gumi (Hausa)
56:65
لَوْ نَشَآءُ لَجَعَلْنَـٰهُ حُطَـٰمًا فَظَلْتُمْ تَفَكَّهُونَ
56:65
Dã Munã so lalle, da Mun sanya shi bũsasshiyar ciyãwa, sai ku yini kunã mãmãkin bãƙin ciki. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:66
إِنَّا لَمُغْرَمُونَ
56:66
(Kunã cẽwa) "Lalle haƙĩƙa an azã mana tãra!" - Abubakar Gumi (Hausa)
56:67
بَلْ نَحْنُ مَحْرُومُونَ
56:67
"Ã'a, mun dai zama waɗanda aka hanã wa!" - Abubakar Gumi (Hausa)
56:68
أَفَرَءَيْتُمُ ٱلْمَآءَ ٱلَّذِى تَشْرَبُونَ
56:68
Shin, kuma kun ga ruwa wannan da kuke sha? - Abubakar Gumi (Hausa)
56:69
ءَأَنتُمْ أَنزَلْتُمُوهُ مِنَ ٱلْمُزْنِ أَمْ نَحْنُ ٱلْمُنزِلُونَ
56:69
Shin, kũ ne kuke saukar da shi daga girgije, kõ kuwa Mũne Mãsu saukarwa? - Abubakar Gumi (Hausa)
56:70
لَوْ نَشَآءُ جَعَلْنَـٰهُ أُجَاجًا فَلَوْلَا تَشْكُرُونَ
56:70
Dã Mun so, dã Mun mayar da shi ruwan zartsi. To don me bã ku gõdẽwa? - Abubakar Gumi (Hausa)
56:71
أَفَرَءَيْتُمُ ٱلنَّارَ ٱلَّتِى تُورُونَ
56:71
Shin, kuma kun ga wutã wannan da kuke ƙyastãwa? - Abubakar Gumi (Hausa)
56:72
ءَأَنتُمْ أَنشَأْتُمْ شَجَرَتَهَآ أَمْ نَحْنُ ٱلْمُنشِـُٔونَ
56:72
Shin, kũ ne kuke ƙagã halittar itãciyarta, kõ kuwa Mũ ne Mãsu ƙãgãwa? - Abubakar Gumi (Hausa)
56:73
نَحْنُ جَعَلْنَـٰهَا تَذْكِرَةً وَمَتَـٰعًا لِّلْمُقْوِينَ
56:73
Mũ ne Muka sanya ta wata abar wa'azi da jin dãɗi ga matafiya a cikin jẽji. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:74
فَسَبِّحْ بِٱسْمِ رَبِّكَ ٱلْعَظِيمِ
56:74
Sai ka tsarkake sũnan Ubangijinka Mai girma. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:75
۞ فَلَآ أُقْسِمُ بِمَوَٰقِعِ ٱلنُّجُومِ
56:75
To, bã sai Na yi rantsuwa ba da lõkutan fãɗuwar taurãri. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:76
وَإِنَّهُۥ لَقَسَمٌ لَّوْ تَعْلَمُونَ عَظِيمٌ
56:76
Kuma lalle ne' haƙĩƙa, rantsuwa ce mai girma, dã kun sani. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:77
إِنَّهُۥ لَقُرْءَانٌ كَرِيمٌ
56:77
Lalle shi (wannan littãfi), haƙĩƙa, abin karantãwa ne mai daraja. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:78
فِى كِتَـٰبٍ مَّكْنُونٍ
56:78
A cikin wani littafi tsararre. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:79
لَّا يَمَسُّهُۥٓ إِلَّا ٱلْمُطَهَّرُونَ
56:79
Bãbu mai shãfa shi fãce waɗanda aka tsarkake. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:80
تَنزِيلٌ مِّن رَّبِّ ٱلْعَـٰلَمِينَ
56:80
Wanda aka saukar ne daga Ubangijin halitta. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:81
أَفَبِهَـٰذَا ٱلْحَدِيثِ أَنتُم مُّدْهِنُونَ
56:81
Shin, to, wannan lãbãrin ne kuke mãsu wulãkantãwa? - Abubakar Gumi (Hausa)
56:82
وَتَجْعَلُونَ رِزْقَكُمْ أَنَّكُمْ تُكَذِّبُونَ
56:82
Kuma kunã sanya arzikinku (game da shi) lalle kũ, ku ƙaryata (shi)? - Abubakar Gumi (Hausa)
56:83
فَلَوْلَآ إِذَا بَلَغَتِ ٱلْحُلْقُومَ
56:83
To, don me idan rai ya kai ga maƙõshi? (Kusa da mutuwa). - Abubakar Gumi (Hausa)
56:84
وَأَنتُمْ حِينَئِذٍ تَنظُرُونَ
56:84
Alhãli kuwa kũ, a lõklcin nan, kunã kallo. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:85
وَنَحْنُ أَقْرَبُ إِلَيْهِ مِنكُمْ وَلَـٰكِن لَّا تُبْصِرُونَ
56:85
Kuma Mũ ne mafi kusanta gare shi daga gare ku, to, amma kũ bã ku gani. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:86
فَلَوْلَآ إِن كُنتُمْ غَيْرَ مَدِينِينَ
56:86
To, don me in dai kun kasance bã waɗanda zã a yi wa sakamako ba? - Abubakar Gumi (Hausa)
56:87
تَرْجِعُونَهَآ إِن كُنتُمْ صَـٰدِقِينَ
56:87
Ku mayar da shi (cikin jikinsa) har idan kun kasance mãsu gaskiya. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:88
فَأَمَّآ إِن كَانَ مِنَ ٱلْمُقَرَّبِينَ
56:88
To, amma idan (mai mutuwar) ya kasance daga makusanta, - Abubakar Gumi (Hausa)
56:89
فَرَوْحٌ وَرَيْحَانٌ وَجَنَّتُ نَعِيمٍ
56:89
Sai hũtawa da kyakkyawan abinci da Aljannar ni'ima. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:90
وَأَمَّآ إِن كَانَ مِنْ أَصْحَـٰبِ ٱلْيَمِينِ
56:90
Kuma amma idan ya kasance daga mazõwa dãma, - Abubakar Gumi (Hausa)
56:91
فَسَلَـٰمٌ لَّكَ مِنْ أَصْحَـٰبِ ٱلْيَمِينِ
56:91
Sai (a ce masa) aminci ya tabbata a gare ka daga mazõwa dãma. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:92
وَأَمَّآ إِن كَانَ مِنَ ٱلْمُكَذِّبِينَ ٱلضَّآلِّينَ
56:92
Kuma amma idan ya kasance daga mãsu ƙaryatãwar, ɓatattun, - Abubakar Gumi (Hausa)
56:93
فَنُزُلٌ مِّنْ حَمِيمٍ
56:93
Sai wata liyãfa ta ruwan zãfi. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:94
وَتَصْلِيَةُ جَحِيمٍ
56:94
Da ƙõnuwa da Jahĩm, - Abubakar Gumi (Hausa)
56:95
إِنَّ هَـٰذَا لَهُوَ حَقُّ ٱلْيَقِينِ
56:95
Lalle wannan, haƙĩƙa, ita ce gaskiya ta yaƙĩni. - Abubakar Gumi (Hausa)
56:96
فَسَبِّحْ بِٱسْمِ رَبِّكَ ٱلْعَظِيمِ
56:96
Sabõda haka, ka tsarkake sũnan Ubangijinka, Mai karimci. - Abubakar Gumi (Hausa)