Selected

Original Text
Abubakar Gumi

Available Translations

44 Ad-Dukhān ٱلدُّخَان

< Previous   59 Āyah   The Smoke      Next >  

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.

44:1 حمٓ
44:1
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ḥ. M̃.

44:2 وَٱلْكِتَـٰبِ ٱلْمُبِينِ
44:2
Abubakar Gumi (Hausa) :
Inã rantsuwa da Littãfi Mabayyani.

44:3 إِنَّآ أَنزَلْنَـٰهُ فِى لَيْلَةٍ مُّبَـٰرَكَةٍ ۚ إِنَّا كُنَّا مُنذِرِينَ
44:3
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne, Mũ, Muka saukar da shi a cikin wani dare mai albarka. Lalle Mũ' Mun kasance Mãsu yin gargaɗi.

44:4 فِيهَا يُفْرَقُ كُلُّ أَمْرٍ حَكِيمٍ
44:4
Abubakar Gumi (Hausa) :
A cikinsa (shi daren) ake rarrabe kõwane umurui bayyananne.

44:5 أَمْرًا مِّنْ عِندِنَآ ۚ إِنَّا كُنَّا مُرْسِلِينَ
44:5
Abubakar Gumi (Hausa) :
Umurni na daga wurinMu. Lalle Mũ ne Muka kasanceMãsu aikãwã.

44:6 رَحْمَةً مِّن رَّبِّكَ ۚ إِنَّهُۥ هُوَ ٱلسَّمِيعُ ٱلْعَلِيمُ
44:6
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sabõda rahama daga Ubangijinka. Lalle Shĩ, Shi ne Mai ji, Mãsani.

44:7 رَبِّ ٱلسَّمَـٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ وَمَا بَيْنَهُمَآ ۖ إِن كُنتُم مُّوقِنِينَ
44:7
Abubakar Gumi (Hausa) :
(Shĩ ne) Ubangijin sammai da ƙasa da abin da ke a tsakãninsu, idan kun kasance mãsu yaƙĩni (za ku gãne haka).

44:8 لَآ إِلَـٰهَ إِلَّا هُوَ يُحْىِۦ وَيُمِيتُ ۖ رَبُّكُمْ وَرَبُّ ءَابَآئِكُمُ ٱلْأَوَّلِينَ
44:8
Abubakar Gumi (Hausa) :
Babu abin bautãwa fãce Shi. Yana rãyarwa Kuma Yana kashẽwa. (Shi ne) Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku na farko.

44:9 بَلْ هُمْ فِى شَكٍّ يَلْعَبُونَ
44:9
Abubakar Gumi (Hausa) :
A'a sũ, sunã wãsã a cikin shakka.

44:10 فَٱرْتَقِبْ يَوْمَ تَأْتِى ٱلسَّمَآءُ بِدُخَانٍ مُّبِينٍ
44:10
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sabõda haka, ka dakata rãnar da sama zã tã zo da hayãƙi bayyananne.

44:11 يَغْشَى ٱلنَّاسَ ۖ هَـٰذَا عَذَابٌ أَلِيمٌ
44:11
Abubakar Gumi (Hausa) :
Yanã rufe mutãne. Wannan wata azãba ce mai raɗaɗi.

44:12 رَّبَّنَا ٱكْشِفْ عَنَّا ٱلْعَذَابَ إِنَّا مُؤْمِنُونَ
44:12
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ya Ubangijinmu! Ka kuranye mana azãba. Lalle Mũ, mãsu ĩmãni ne.

44:13 أَنَّىٰ لَهُمُ ٱلذِّكْرَىٰ وَقَدْ جَآءَهُمْ رَسُولٌ مُّبِينٌ
44:13
Abubakar Gumi (Hausa) :
Inã tunãwa take a gare su, alhãli kuwa, haƙĩƙa, Manzo mai bayyanãwa Ya je musu (da gargaɗin saukar azãbar, ba su karɓa ba)?

44:14 ثُمَّ تَوَلَّوْا۟ عَنْهُ وَقَالُوا۟ مُعَلَّمٌ مَّجْنُونٌ
44:14
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan suka jũya baya daga gare shi, Kuma suka ce: "Wanda ake gayãwa ne, mahaukaci."

44:15 إِنَّا كَاشِفُوا۟ ٱلْعَذَابِ قَلِيلًا ۚ إِنَّكُمْ عَآئِدُونَ
44:15
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle Mũ, Mãsu kuranyẽwar azãba ne, a ɗan lõkaci kaɗan, lalle kũ, mãsu kõmãwa ne (ga laifin).

44:16 يَوْمَ نَبْطِشُ ٱلْبَطْشَةَ ٱلْكُبْرَىٰٓ إِنَّا مُنتَقِمُونَ
44:16
Abubakar Gumi (Hausa) :
Rãnar da Muke damƙa, damƙa mafi girma, lalle ne Mũ mãsu azãbar rãmuwa ne.

44:17 ۞ وَلَقَدْ فَتَنَّا قَبْلَهُمْ قَوْمَ فِرْعَوْنَ وَجَآءَهُمْ رَسُولٌ كَرِيمٌ
44:17
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma lalle ne haƙĩƙa a gabaninsu, Mun fitini mutãnen Fir'auna, kuma wani Manzo karĩmi ya jẽ musu.

44:18 أَنْ أَدُّوٓا۟ إِلَىَّ عِبَادَ ٱللَّهِ ۖ إِنِّى لَكُمْ رَسُولٌ أَمِينٌ
44:18
Abubakar Gumi (Hausa) :
(Mazon ya ce): "Ku kãwo mini (ĩmãninku) ya bayin Allah! Lalle ni, Manzo ne amintacce zuwa gare ku."

44:19 وَأَن لَّا تَعْلُوا۟ عَلَى ٱللَّهِ ۖ إِنِّىٓ ءَاتِيكُم بِسُلْطَـٰنٍ مُّبِينٍ
44:19
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma kada ku nẽmi ɗaukaka a kan Allah. Lalle nĩ mai zo muku ne da dalĩli bayyananne."

44:20 وَإِنِّى عُذْتُ بِرَبِّى وَرَبِّكُمْ أَن تَرْجُمُونِ
44:20
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma lalle nĩ na nẽmi tsari da Ubangijĩna, kuma Ubangijinku, dõmin kada ku jẽfe ni."

44:21 وَإِن لَّمْ تُؤْمِنُوا۟ لِى فَٱعْتَزِلُونِ
44:21
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma idan ba ku yi ĩmãni sabõda nĩ ba, to, ku nĩsance ni."

44:22 فَدَعَا رَبَّهُۥٓ أَنَّ هَـٰٓؤُلَآءِ قَوْمٌ مُّجْرِمُونَ
44:22
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai ya kirayi Ubangjinsa cẽwa waɗannan mutãnene mãsu laifi.

44:23 فَأَسْرِ بِعِبَادِى لَيْلًا إِنَّكُم مُّتَّبَعُونَ
44:23
Abubakar Gumi (Hausa) :
(Allah Ya ce): "To, ka yi tafiyar dare da bayiNa, da dare. Lalle kũ, waɗanda ake bĩ ne (dõmin a kãma ku.)"

44:24 وَٱتْرُكِ ٱلْبَحْرَ رَهْوًا ۖ إِنَّهُمْ جُندٌ مُّغْرَقُونَ
44:24
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma ka bar tẽku rarrabe. Lalle sũ, runduna ce abar nutsarwa."

44:25 كَمْ تَرَكُوا۟ مِن جَنَّـٰتٍ وَعُيُونٍ
44:25
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da yawa suka bar gõnaki da marẽmari.

44:26 وَزُرُوعٍ وَمَقَامٍ كَرِيمٍ
44:26
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da shuke-shuke da matsayi mai kyau.

44:27 وَنَعْمَةٍ كَانُوا۟ فِيهَا فَـٰكِهِينَ
44:27
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da wata ni'ima da suka kasance a cikinta sunã mãsu hutu.

44:28 كَذَٰلِكَ ۖ وَأَوْرَثْنَـٰهَا قَوْمًا ءَاخَرِينَ
44:28
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kamar haka! Kuma Muka gãdar da ita ga waɗansu mutãne na dabam.

44:29 فَمَا بَكَتْ عَلَيْهِمُ ٱلسَّمَآءُ وَٱلْأَرْضُ وَمَا كَانُوا۟ مُنظَرِينَ
44:29
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan samã da ƙasã ba su yi kũka a kansu ba, Kuma ba su kasance waɗanda ake yi wa jinkiri ba.

44:30 وَلَقَدْ نَجَّيْنَا بَنِىٓ إِسْرَٰٓءِيلَ مِنَ ٱلْعَذَابِ ٱلْمُهِينِ
44:30
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma lalle ne, haƙĩƙa Mun tsĩrar da Banĩ Isrã'ĩla daga, azãba mai wulãkantãwa.

44:31 مِن فِرْعَوْنَ ۚ إِنَّهُۥ كَانَ عَالِيًا مِّنَ ٱلْمُسْرِفِينَ
44:31
Abubakar Gumi (Hausa) :
Daga Fir'auna. Lalle shi, ya kasance maɗaukaki daga cikin mãsu ɓarna.

44:32 وَلَقَدِ ٱخْتَرْنَـٰهُمْ عَلَىٰ عِلْمٍ عَلَى ٱلْعَـٰلَمِينَ
44:32
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun zãɓe su sabõda wani ilmi (na Taurata) a kan mutãne.

44:33 وَءَاتَيْنَـٰهُم مِّنَ ٱلْـَٔايَـٰتِ مَا فِيهِ بَلَـٰٓؤٌا۟ مُّبِينٌ
44:33
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma Muka bã su, daga ãyõyin mu'ujizõji, abin da yake a cikinsa, akwai ni'ima bayyananna

44:34 إِنَّ هَـٰٓؤُلَآءِ لَيَقُولُونَ
44:34
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle waɗannan mutãne, haƙĩka, sunã cẽwa,

44:35 إِنْ هِىَ إِلَّا مَوْتَتُنَا ٱلْأُولَىٰ وَمَا نَحْنُ بِمُنشَرِينَ
44:35
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Babu wani abu sai mutuwarmu ta farko, kuma ba mu zama waɗanda ake tãyarwa ba."

44:36 فَأْتُوا۟ بِـَٔابَآئِنَآ إِن كُنتُمْ صَـٰدِقِينَ
44:36
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Sai ku zo da ubanninmu, idan kun kasance mãsu gaskiya."

44:37 أَهُمْ خَيْرٌ أَمْ قَوْمُ تُبَّعٍ وَٱلَّذِينَ مِن قَبْلِهِمْ ۚ أَهْلَكْنَـٰهُمْ ۖ إِنَّهُمْ كَانُوا۟ مُجْرِمِينَ
44:37
Abubakar Gumi (Hausa) :
shin, sũ ne mafĩfĩta kõ kuwa mutãnen Tubba'u, kuma da waɗanda ke a gabãninsu? Mun halaka su, lalle sũ, sun kasance mãsu laifi.

44:38 وَمَا خَلَقْنَا ٱلسَّمَـٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضَ وَمَا بَيْنَهُمَا لَـٰعِبِينَ
44:38
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma ba Mu halitta slmmai da ƙasa da abin da ke a tsakãninsu ba, alhãli kuwa Munã mãsu wãsã.

44:39 مَا خَلَقْنَـٰهُمَآ إِلَّا بِٱلْحَقِّ وَلَـٰكِنَّ أَكْثَرَهُمْ لَا يَعْلَمُونَ
44:39
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ba Mu halitta su ba fãce da manufa ta gaskiya, kuma amma mafi yawansu, ba su sani ba.

44:40 إِنَّ يَوْمَ ٱلْفَصْلِ مِيقَـٰتُهُمْ أَجْمَعِينَ
44:40
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle rãnar rarrabẽwa, ita ce lõkacin wa'adinsu gabã ɗaya.

44:41 يَوْمَ لَا يُغْنِى مَوْلًى عَن مَّوْلًى شَيْـًٔا وَلَا هُمْ يُنصَرُونَ
44:41
Abubakar Gumi (Hausa) :
Rãnar da wani zumu bã ya amfãnin wani zumu da kõme kuma ba su zama anã taimakon su ba.

44:42 إِلَّا مَن رَّحِمَ ٱللَّهُ ۚ إِنَّهُۥ هُوَ ٱلْعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ
44:42
Abubakar Gumi (Hausa) :
fãce wanda Allah Ya yi wa rahama. Lalle Shi (Allah), shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.

44:43 إِنَّ شَجَرَتَ ٱلزَّقُّومِ
44:43
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle itãciyar zaƙƙũm (ɗanyen wutã),

44:44 طَعَامُ ٱلْأَثِيمِ
44:44
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ita ce abincin mai laifi.

44:45 كَٱلْمُهْلِ يَغْلِى فِى ٱلْبُطُونِ
44:45
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kamar narkakken kwalta yanã tafasa a cikin cikunna.

44:46 كَغَلْىِ ٱلْحَمِيمِ
44:46
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kamar tafasar ruwan zãfi.

44:47 خُذُوهُ فَٱعْتِلُوهُ إِلَىٰ سَوَآءِ ٱلْجَحِيمِ
44:47
Abubakar Gumi (Hausa) :
(A cẽ wa malã'ikun wutã), "Ku kãmã shi, sa'an nan ku fizge shi zuwa ga tsakiyar Jahĩm."

44:48 ثُمَّ صُبُّوا۟ فَوْقَ رَأْسِهِۦ مِنْ عَذَابِ ٱلْحَمِيمِ
44:48
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Sa'an nan ku zuba, a kansa, daga azãbar ruwan zãfi."

44:49 ذُقْ إِنَّكَ أَنتَ ٱلْعَزِيزُ ٱلْكَرِيمُ
44:49
Abubakar Gumi (Hausa) :
(A ce masã), "Ka ɗanɗana! Lalle kai, kai ne mabuwãyi mai girma!"

44:50 إِنَّ هَـٰذَا مَا كُنتُم بِهِۦ تَمْتَرُونَ
44:50
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Lalle wannan, shi ne abin da kuka kasance kunã shakka game da shi."

44:51 إِنَّ ٱلْمُتَّقِينَ فِى مَقَامٍ أَمِينٍ
44:51
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle mãsu taƙawa sunã cikin matsayi amintacce.

44:52 فِى جَنَّـٰتٍ وَعُيُونٍ
44:52
Abubakar Gumi (Hausa) :
A cikin gidãjen Aljanna da marẽmari.

44:53 يَلْبَسُونَ مِن سُندُسٍ وَإِسْتَبْرَقٍ مُّتَقَـٰبِلِينَ
44:53
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sunã tufanta daga tufãfin alharĩni raƙĩƙi, da mai kauri, sunã mãsu zaman fuskantar jũna.

44:54 كَذَٰلِكَ وَزَوَّجْنَـٰهُم بِحُورٍ عِينٍ
44:54
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kamar haka, kuma Mun aurar da su da mãtã mãsu kyaun idãnu, mãsu girmansu.

44:55 يَدْعُونَ فِيهَا بِكُلِّ فَـٰكِهَةٍ ءَامِنِينَ
44:55
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sunã kira, a cikinsu (gidẽjen) ga dukan 'ya'yan itãcen marmari, sunã amintattu (daga dukan abin tsõro).

44:56 لَا يَذُوقُونَ فِيهَا ٱلْمَوْتَ إِلَّا ٱلْمَوْتَةَ ٱلْأُولَىٰ ۖ وَوَقَىٰهُمْ عَذَابَ ٱلْجَحِيمِ
44:56
Abubakar Gumi (Hausa) :
Bã su ɗanɗanar mutuwa, a cikinsu, fãce mutuwar farko, kuma (Allah), Ya tsare musu azãbar Jahĩm.

44:57 فَضْلًا مِّن رَّبِّكَ ۚ ذَٰلِكَ هُوَ ٱلْفَوْزُ ٱلْعَظِيمُ
44:57
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sabõda falala daga Ubangijinka. Wancan shi ne babban rabo, mai girma.

44:58 فَإِنَّمَا يَسَّرْنَـٰهُ بِلِسَانِكَ لَعَلَّهُمْ يَتَذَكَّرُونَ
44:58
Abubakar Gumi (Hausa) :
Dõmin haka kawai Muka sauƙaƙar da shi (Alƙur'ãni) da harshenka, tsammãninsu, su riƙa tunãwa.

44:59 فَٱرْتَقِبْ إِنَّهُم مُّرْتَقِبُونَ
44:59
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai ka yi jira. Lalle sũ, mãsu jira ne.