Selected
Original Text
Abubakar Gumi
Abdullah Yusuf Ali
Abdul Majid Daryabadi
Abul Ala Maududi
Ahmed Ali
Ahmed Raza Khan
A. J. Arberry
Ali Quli Qarai
Hasan al-Fatih Qaribullah and Ahmad Darwish
Mohammad Habib Shakir
Mohammed Marmaduke William Pickthall
Muhammad Sarwar
Muhammad Taqi-ud-Din al-Hilali and Muhammad Muhsin Khan
Safi-ur-Rahman al-Mubarakpuri
Saheeh International
Talal Itani
Transliteration
Wahiduddin Khan
بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.
84:1
إِذَا ٱلسَّمَآءُ ٱنشَقَّتْ
84:1
Idan sama ta kẽce, - Abubakar Gumi (Hausa)
84:2
وَأَذِنَتْ لِرَبِّهَا وَحُقَّتْ
84:2
Ta saurari Ubangijinta, kuma aka wajabta mata yin saurãron, - Abubakar Gumi (Hausa)
84:3
وَإِذَا ٱلْأَرْضُ مُدَّتْ
84:3
Kuma idan ƙasã aka mĩƙe ta, - Abubakar Gumi (Hausa)
84:4
وَأَلْقَتْ مَا فِيهَا وَتَخَلَّتْ
84:4
Kuma ta jẽfar da abin da yake a cikinta, tã wõfinta daga kõme. - Abubakar Gumi (Hausa)
84:5
وَأَذِنَتْ لِرَبِّهَا وَحُقَّتْ
84:5
Kuma ta saurãri Ubangijinta, aka wajabta mata yin saurãren, - Abubakar Gumi (Hausa)
84:6
يَـٰٓأَيُّهَا ٱلْإِنسَـٰنُ إِنَّكَ كَادِحٌ إِلَىٰ رَبِّكَ كَدْحًا فَمُلَـٰقِيهِ
84:6
Ya kai mutum! Lalle ne kai mai aikin wahal da kai ne zuwa ga Ubangijinka, wahala mai tsanani, To, kai mai haɗuwa da Shi ne. - Abubakar Gumi (Hausa)
84:7
فَأَمَّا مَنْ أُوتِىَ كِتَـٰبَهُۥ بِيَمِينِهِۦ
84:7
To, amma wanda aka bai wa littãfinsa da damansa. - Abubakar Gumi (Hausa)
84:8
فَسَوْفَ يُحَاسَبُ حِسَابًا يَسِيرًا
84:8
To, za a yi masa hisãbi, hisãbi mai sauƙi. - Abubakar Gumi (Hausa)
84:9
وَيَنقَلِبُ إِلَىٰٓ أَهْلِهِۦ مَسْرُورًا
84:9
Kuma ya jũya zuwa ga iyãlinsa (a cikin Aljanna), yanã mai raha. - Abubakar Gumi (Hausa)
84:10
وَأَمَّا مَنْ أُوتِىَ كِتَـٰبَهُۥ وَرَآءَ ظَهْرِهِۦ
84:10
Kuma amma wanda aka bai wa littãfinsa, daga wajen bãyansa. - Abubakar Gumi (Hausa)
84:11
فَسَوْفَ يَدْعُوا۟ ثُبُورًا
84:11
To, zã shi dinga kiran halaka! - Abubakar Gumi (Hausa)
84:12
وَيَصْلَىٰ سَعِيرًا
84:12
Kuma ya shiga sa'ĩr. - Abubakar Gumi (Hausa)
84:13
إِنَّهُۥ كَانَ فِىٓ أَهْلِهِۦ مَسْرُورًا
84:13
Lal1e ne shi, yã kasance (a dũniya) cikin iyãlinsa yanã mai raha. - Abubakar Gumi (Hausa)
84:14
إِنَّهُۥ ظَنَّ أَن لَّن يَحُورَ
84:14
Lalle ne yã yi zaton bã zai kõmo ba. - Abubakar Gumi (Hausa)
84:15
بَلَىٰٓ إِنَّ رَبَّهُۥ كَانَ بِهِۦ بَصِيرًا
84:15
Na'am! Lalle ne, Ubangijinsa Ya kasance Mai gani gare shi. - Abubakar Gumi (Hausa)
84:16
فَلَآ أُقْسِمُ بِٱلشَّفَقِ
84:16
To, ba sai Nã rantse da shafaƙi ba. - Abubakar Gumi (Hausa)
84:17
وَٱلَّيْلِ وَمَا وَسَقَ
84:17
Da dare, da abin da ya ƙunsa. - Abubakar Gumi (Hausa)
84:18
وَٱلْقَمَرِ إِذَا ٱتَّسَقَ
84:18
Da watã idan (haskensa) ya cika. - Abubakar Gumi (Hausa)
84:19
لَتَرْكَبُنَّ طَبَقًا عَن طَبَقٍ
84:19
Lalle ne kunã hawan wani hãli daga wani hãli. - Abubakar Gumi (Hausa)
84:20
فَمَا لَهُمْ لَا يُؤْمِنُونَ
84:20
To, mẽ ya sãme su, ba su yin ĩmãni? - Abubakar Gumi (Hausa)
84:21
وَإِذَا قُرِئَ عَلَيْهِمُ ٱلْقُرْءَانُ لَا يَسْجُدُونَ ۩
84:21
Kuma idan an karanta Alkur'ãni a kansu, bã su yin tawãli'u? - Abubakar Gumi (Hausa)
84:22
بَلِ ٱلَّذِينَ كَفَرُوا۟ يُكَذِّبُونَ
84:22
Ba haka ba! waɗanda suka kãfirta, sai ƙaryatãwa suke yi. - Abubakar Gumi (Hausa)
84:23
وَٱللَّهُ أَعْلَمُ بِمَا يُوعُونَ
84:23
Alhãli Allah Shĩ ne Mafi sani ga abin a suke tãrãwa. - Abubakar Gumi (Hausa)
84:24
فَبَشِّرْهُم بِعَذَابٍ أَلِيمٍ
84:24
Saboda haka, ka yi musu bushãra da azãba mai raɗaɗi. - Abubakar Gumi (Hausa)
84:25
إِلَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ وَعَمِلُوا۟ ٱلصَّـٰلِحَـٰتِ لَهُمْ أَجْرٌ غَيْرُ مَمْنُونٍۭ
84:25
Fãce waɗanda suka yi ĩmãni, suka aikata ayyukan ƙwarai, sunã da wani sakamako wanda bã ya yankẽwa. - Abubakar Gumi (Hausa)