Selected
Original Text
Abubakar Gumi
Abdullah Yusuf Ali
Abdul Majid Daryabadi
Abul Ala Maududi
Ahmed Ali
Ahmed Raza Khan
A. J. Arberry
Ali Quli Qarai
Hasan al-Fatih Qaribullah and Ahmad Darwish
Mohammad Habib Shakir
Mohammed Marmaduke William Pickthall
Muhammad Sarwar
Muhammad Taqi-ud-Din al-Hilali and Muhammad Muhsin Khan
Safi-ur-Rahman al-Mubarakpuri
Saheeh International
Talal Itani
Transliteration
Wahiduddin Khan
بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.
68:1
نٓ ۚ وَٱلْقَلَمِ وَمَا يَسْطُرُونَ
68:1
Ñ. Na rantse da alƙalami da abin da (marubũta) suke rubũtãwa. - Abubakar Gumi (Hausa)
68:2
مَآ أَنتَ بِنِعْمَةِ رَبِّكَ بِمَجْنُونٍ
68:2
Kai, sabõda ni'imar Ubangijinka, bã mahaukaci kake ba. - Abubakar Gumi (Hausa)
68:3
وَإِنَّ لَكَ لَأَجْرًا غَيْرَ مَمْنُونٍ
68:3
Kuma, lalle, haƙĩƙa kanã da lãdar da bã ta yankewa. - Abubakar Gumi (Hausa)
68:4
وَإِنَّكَ لَعَلَىٰ خُلُقٍ عَظِيمٍ
68:4
Kuma, lalle haƙiƙa kana a kan hãlãyen kirki, manya. - Abubakar Gumi (Hausa)
68:5
فَسَتُبْصِرُ وَيُبْصِرُونَ
68:5
Don haka, zã ka gani, sũ kuma zã su gani. - Abubakar Gumi (Hausa)
68:6
بِأَييِّكُمُ ٱلْمَفْتُونُ
68:6
Ga wanenku haukã take. - Abubakar Gumi (Hausa)
68:7
إِنَّ رَبَّكَ هُوَ أَعْلَمُ بِمَن ضَلَّ عَن سَبِيلِهِۦ وَهُوَ أَعْلَمُ بِٱلْمُهْتَدِينَ
68:7
Lalle Ubangijinka Shi ne Mafi sani ga wanda ya ɓace daga tafarkinSa. Kuma Shi ne Mafi sani ga mãsu shiryuwa. - Abubakar Gumi (Hausa)
68:8
فَلَا تُطِعِ ٱلْمُكَذِّبِينَ
68:8
Saboda haka kada ka bi mãsu ƙaryatãwa. - Abubakar Gumi (Hausa)
68:9
وَدُّوا۟ لَوْ تُدْهِنُ فَيُدْهِنُونَ
68:9
Sunã fatar ka sassauta, su kuma sũ sassauta. - Abubakar Gumi (Hausa)
68:10
وَلَا تُطِعْ كُلَّ حَلَّافٍ مَّهِينٍ
68:10
Kada ka bi dukkan mai yawan rantsuwa, walãkantacce. - Abubakar Gumi (Hausa)
68:11
هَمَّازٍ مَّشَّآءٍۭ بِنَمِيمٍ
68:11
Mai zunɗe, mai yãwo da gulma. - Abubakar Gumi (Hausa)
68:12
مَّنَّاعٍ لِّلْخَيْرِ مُعْتَدٍ أَثِيمٍ
68:12
Mai hana alhẽri mai zãlunci, mai zunubi. - Abubakar Gumi (Hausa)
68:13
عُتُلٍّۭ بَعْدَ ذَٰلِكَ زَنِيمٍ
68:13
Mai girman kai, bãyan haka kuma la'ĩmi (bã ya son alhẽri). - Abubakar Gumi (Hausa)
68:14
أَن كَانَ ذَا مَالٍ وَبَنِينَ
68:14
Sabõda yã kasance mai dũkiya da ɗiya. - Abubakar Gumi (Hausa)
68:15
إِذَا تُتْلَىٰ عَلَيْهِ ءَايَـٰتُنَا قَالَ أَسَـٰطِيرُ ٱلْأَوَّلِينَ
68:15
Idan ana karanta masa ãyõyinMu, sai ya ce: "Tatsũniyõyin mutãnen farko ne." - Abubakar Gumi (Hausa)
68:16
سَنَسِمُهُۥ عَلَى ٱلْخُرْطُومِ
68:16
Zã Mu yi masa alãma a kan hanci. - Abubakar Gumi (Hausa)
68:17
إِنَّا بَلَوْنَـٰهُمْ كَمَا بَلَوْنَآ أَصْحَـٰبَ ٱلْجَنَّةِ إِذْ أَقْسَمُوا۟ لَيَصْرِمُنَّهَا مُصْبِحِينَ
68:17
Lalle Mun jarrabe su kamar yadda Muka jarrabi mãsu gonar lambu, a lokacin da suka yi rantsuwa, wai lalle zã su girbe amfãninta, suna mãsu asubanci. - Abubakar Gumi (Hausa)
68:18
وَلَا يَسْتَثْنُونَ
68:18
Kuma (suka yi niyya), bã su kõ tõgẽwa. - Abubakar Gumi (Hausa)
68:19
فَطَافَ عَلَيْهَا طَآئِفٌ مِّن رَّبِّكَ وَهُمْ نَآئِمُونَ
68:19
Wani mai kẽwayãwa daga Ubangijinka ya kẽwayã a kanta, (ya ƙone ta,) alhãli sunã barci. - Abubakar Gumi (Hausa)
68:20
فَأَصْبَحَتْ كَٱلصَّرِيمِ
68:20
Sai ta wãyi gari (baƙa ƙirin) kamar dare. - Abubakar Gumi (Hausa)
68:21
فَتَنَادَوْا۟ مُصْبِحِينَ
68:21
Sai suka kirãyi jũna, sunã mãsu yin asubanci. - Abubakar Gumi (Hausa)
68:22
أَنِ ٱغْدُوا۟ عَلَىٰ حَرْثِكُمْ إِن كُنتُمْ صَـٰرِمِينَ
68:22
Cẽwa ku yi sammakõ ga amfãnin gõnarku, idan kun kasance mãsu girbewa. - Abubakar Gumi (Hausa)
68:23
فَٱنطَلَقُوا۟ وَهُمْ يَتَخَـٰفَتُونَ
68:23
Sai suka tafi sunã shãwara a ɓõye (sunã cẽwa). - Abubakar Gumi (Hausa)
68:24
أَن لَّا يَدْخُلَنَّهَا ٱلْيَوْمَ عَلَيْكُم مِّسْكِينٌ
68:24
"Lalle kada wani miskĩni ya shigar muku ita a yau!" - Abubakar Gumi (Hausa)
68:25
وَغَدَوْا۟ عَلَىٰ حَرْدٍ قَـٰدِرِينَ
68:25
Kuma suka yi sammako akan (niyyar) rõwa, matuƙar iyãwarsu. - Abubakar Gumi (Hausa)
68:26
فَلَمَّا رَأَوْهَا قَالُوٓا۟ إِنَّا لَضَآلُّونَ
68:26
Lõkacin da suka gan ta, sai suka ce: "Lalle, mun saki hanya (mun ɓace)!" - Abubakar Gumi (Hausa)
68:27
بَلْ نَحْنُ مَحْرُومُونَ
68:27
"Ba haka ba, mũ dai, an hana mu ne." - Abubakar Gumi (Hausa)
68:28
قَالَ أَوْسَطُهُمْ أَلَمْ أَقُل لَّكُمْ لَوْلَا تُسَبِّحُونَ
68:28
Mafificinsu (hankali) ya ce: "Ban gaya muku ba, yã kamata ku tsarkake Allah?" - Abubakar Gumi (Hausa)
68:29
قَالُوا۟ سُبْحَـٰنَ رَبِّنَآ إِنَّا كُنَّا ظَـٰلِمِينَ
68:29
Suka ce: "Tsarki ya tabbata ga Ubangijinmu! Lalle, mu mun kasance azzãlumai." - Abubakar Gumi (Hausa)
68:30
فَأَقْبَلَ بَعْضُهُمْ عَلَىٰ بَعْضٍ يَتَلَـٰوَمُونَ
68:30
Sai suka fuskanci jũna, sunã zargin kansu. - Abubakar Gumi (Hausa)
68:31
قَالُوا۟ يَـٰوَيْلَنَآ إِنَّا كُنَّا طَـٰغِينَ
68:31
Suka ce: "Kaitonmu! Lalle, mũ ne muka kasance mãsu ƙẽtare iyãka." - Abubakar Gumi (Hausa)
68:32
عَسَىٰ رَبُّنَآ أَن يُبْدِلَنَا خَيْرًا مِّنْهَآ إِنَّآ إِلَىٰ رَبِّنَا رَٰغِبُونَ
68:32
"Mai yiwuwa ne Ubangijinmu Ya musanya mana da wani abu da yã fi ta. Lalle, mũ (ba mu yanke ƙauna ba) zuwa ga Ubangijinmu, mãsu kwaɗayi ne." - Abubakar Gumi (Hausa)
68:33
كَذَٰلِكَ ٱلْعَذَابُ ۖ وَلَعَذَابُ ٱلْـَٔاخِرَةِ أَكْبَرُ ۚ لَوْ كَانُوا۟ يَعْلَمُونَ
68:33
Haka dai azãbar take, kuma lalle ne azãbar Lãhira ta fi girma, in da sun kasance zã su iya gãnẽwã. - Abubakar Gumi (Hausa)
68:34
إِنَّ لِلْمُتَّقِينَ عِندَ رَبِّهِمْ جَنَّـٰتِ ٱلنَّعِيمِ
68:34
Lalle ne mãsu taƙawa nã da a wurin Ubangijinsu, gidãjen Aljanna na ni'ima. - Abubakar Gumi (Hausa)
68:35
أَفَنَجْعَلُ ٱلْمُسْلِمِينَ كَٱلْمُجْرِمِينَ
68:35
Shin ko zã Mu sanya waɗanda ke bi da ɗa'a kamar mãsu laifi? - Abubakar Gumi (Hausa)
68:36
مَا لَكُمْ كَيْفَ تَحْكُمُونَ
68:36
Me ya sãme ku, yãya kuke yin hukunci (da haka)? - Abubakar Gumi (Hausa)
68:37
أَمْ لَكُمْ كِتَـٰبٌ فِيهِ تَدْرُسُونَ
68:37
Ko kuna da wani littafi, wanda a cikinsa, kuke karantãwa? - Abubakar Gumi (Hausa)
68:38
إِنَّ لَكُمْ فِيهِ لَمَا تَخَيَّرُونَ
68:38
Cẽwã kunã da, a cikinsa lalle (duk) abin da rãyukanku suka zãɓa? - Abubakar Gumi (Hausa)
68:39
أَمْ لَكُمْ أَيْمَـٰنٌ عَلَيْنَا بَـٰلِغَةٌ إِلَىٰ يَوْمِ ٱلْقِيَـٰمَةِ ۙ إِنَّ لَكُمْ لَمَا تَحْكُمُونَ
68:39
Kõ kunã (riƙe) da wasu rantsuwõyin alkawari a kanMu, har ya zuwa Rãnar ¡iyãma, cẽwa lalle ne kunã da abin da kuke hukuntã wa kanku? - Abubakar Gumi (Hausa)
68:40
سَلْهُمْ أَيُّهُم بِذَٰلِكَ زَعِيمٌ
68:40
Ka tambaye su, wãne, a cikinsu, ke lãmuncewã ga sãmun wannan (hukuncin)? - Abubakar Gumi (Hausa)
68:41
أَمْ لَهُمْ شُرَكَآءُ فَلْيَأْتُوا۟ بِشُرَكَآئِهِمْ إِن كَانُوا۟ صَـٰدِقِينَ
68:41
Kõ sunã da abõkan tãrẽwa (ga wannan ra'ayi)? To, sai su kãwo abõkan tãrayyarsu, idan sun kasance mãsu gaskiya. - Abubakar Gumi (Hausa)
68:42
يَوْمَ يُكْشَفُ عَن سَاقٍ وَيُدْعَوْنَ إِلَى ٱلسُّجُودِ فَلَا يَسْتَطِيعُونَ
68:42
Ranar da zã a kuranye ƙwabri, kuma a kira su zuwa ga yin sujũda, sai bã zã su iyãwa ba. - Abubakar Gumi (Hausa)
68:43
خَـٰشِعَةً أَبْصَـٰرُهُمْ تَرْهَقُهُمْ ذِلَّةٌ ۖ وَقَدْ كَانُوا۟ يُدْعَوْنَ إِلَى ٱلسُّجُودِ وَهُمْ سَـٰلِمُونَ
68:43
Su fito da idãnu ƙasƙantattu, wulãkanci yana rufe su. Lalle ne a dã sun kasance anã kiran su zuwa, yin sujũdar, alhãli kuwa sunã lãfiya lau, (suka ƙi yi). - Abubakar Gumi (Hausa)
68:44
فَذَرْنِى وَمَن يُكَذِّبُ بِهَـٰذَا ٱلْحَدِيثِ ۖ سَنَسْتَدْرِجُهُم مِّنْ حَيْثُ لَا يَعْلَمُونَ
68:44
Sabõda haka ka bar Ni da mai ƙaryata wanna lãbãri (Alƙur'ãni). Zã Mu yi musu istidrãji daga inda ba su sani ba. - Abubakar Gumi (Hausa)
68:45
وَأُمْلِى لَهُمْ ۚ إِنَّ كَيْدِى مَتِينٌ
68:45
Ina jinkirtã musu, lalle kaidiNa mai ƙarfi ne. - Abubakar Gumi (Hausa)
68:46
أَمْ تَسْـَٔلُهُمْ أَجْرًا فَهُم مِّن مَّغْرَمٍ مُّثْقَلُونَ
68:46
Kõ kana tambayar su wata la'ada ne, sabõda haka sũ, daga wannan tãrar, suke jin an nauyaya musu? - Abubakar Gumi (Hausa)
68:47
أَمْ عِندَهُمُ ٱلْغَيْبُ فَهُمْ يَكْتُبُونَ
68:47
Ko kuma sunã da ilmin gaibu ne, wãto sunã yin rubũtun (abin da suke faɗã daga gare shi) ne? - Abubakar Gumi (Hausa)
68:48
فَٱصْبِرْ لِحُكْمِ رَبِّكَ وَلَا تَكُن كَصَاحِبِ ٱلْحُوتِ إِذْ نَادَىٰ وَهُوَ مَكْظُومٌ
68:48
Sabõda haka, ka yi haƙuri da hukuncin Ubangijinka, kada ka zama kamar Ma'abũcin kĩfi, alõkacin da ya yi kira, alhãli yana cike da hushi. - Abubakar Gumi (Hausa)
68:49
لَّوْلَآ أَن تَدَٰرَكَهُۥ نِعْمَةٌ مِّن رَّبِّهِۦ لَنُبِذَ بِٱلْعَرَآءِ وَهُوَ مَذْمُومٌ
68:49
Ba dõmin ni'ima daga wajen Ubangijinsa tã riske shi ba, lalle ne da an jẽfa shi a cikin wõfintacciyar ƙasa, alhãli yanã abin zargi. - Abubakar Gumi (Hausa)
68:50
فَٱجْتَبَـٰهُ رَبُّهُۥ فَجَعَلَهُۥ مِنَ ٱلصَّـٰلِحِينَ
68:50
Sai Ubangijinsa Ya zãɓe shi, sa'an nan Ya sanya shi a cikin mutãnen kirki. - Abubakar Gumi (Hausa)
68:51
وَإِن يَكَادُ ٱلَّذِينَ كَفَرُوا۟ لَيُزْلِقُونَكَ بِأَبْصَـٰرِهِمْ لَمَّا سَمِعُوا۟ ٱلذِّكْرَ وَيَقُولُونَ إِنَّهُۥ لَمَجْنُونٌ
68:51
Kuma lalle, ne waɗanda suka kãfirta sunã yin kamar su kãyar da kai sabõ da kallonsu (kallon mãmãki), a lokacin da suke jin karãtun Alƙur'ãni, kuma sunã cẽwa, "Lalle ne shi mahaukaci ne!" - Abubakar Gumi (Hausa)
68:52
وَمَا هُوَ إِلَّا ذِكْرٌ لِّلْعَـٰلَمِينَ
68:52
Shi (Alƙur'ãni) bai kasance ba, fãce abin tunãtarwa ne ga duka dũniya. - Abubakar Gumi (Hausa)