Selected
Original Text
Abubakar Gumi
Abdullah Yusuf Ali
Abdul Majid Daryabadi
Abul Ala Maududi
Ahmed Ali
Ahmed Raza Khan
A. J. Arberry
Ali Quli Qarai
Hasan al-Fatih Qaribullah and Ahmad Darwish
Mohammad Habib Shakir
Mohammed Marmaduke William Pickthall
Muhammad Sarwar
Muhammad Taqi-ud-Din al-Hilali and Muhammad Muhsin Khan
Safi-ur-Rahman al-Mubarakpuri
Saheeh International
Talal Itani
Transliteration
Wahiduddin Khan
بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.
92:1
وَٱلَّيْلِ إِذَا يَغْشَىٰ
92:1
Inã rantsuwa da dare a lõkacin da yake rufẽwa. - Abubakar Gumi (Hausa)
92:2
وَٱلنَّهَارِ إِذَا تَجَلَّىٰ
92:2
Da yini a lõkacin da yake kuranyẽwa. - Abubakar Gumi (Hausa)
92:3
وَمَا خَلَقَ ٱلذَّكَرَ وَٱلْأُنثَىٰٓ
92:3
Da abin da ya halitta namiji da mace. - Abubakar Gumi (Hausa)
92:4
إِنَّ سَعْيَكُمْ لَشَتَّىٰ
92:4
Lãlle ne ayyukanku, dabam-dabam suke. - Abubakar Gumi (Hausa)
92:5
فَأَمَّا مَنْ أَعْطَىٰ وَٱتَّقَىٰ
92:5
To, amma wanda ya yi kyauta, kuma ya yi taƙawa. - Abubakar Gumi (Hausa)
92:6
وَصَدَّقَ بِٱلْحُسْنَىٰ
92:6
Kuma ya gaskata kalma mai kyãwo. - Abubakar Gumi (Hausa)
92:7
فَسَنُيَسِّرُهُۥ لِلْيُسْرَىٰ
92:7
To, zã Mu sauƙaƙe masa har ya kai ga sauƙi. - Abubakar Gumi (Hausa)
92:8
وَأَمَّا مَنۢ بَخِلَ وَٱسْتَغْنَىٰ
92:8
Kuma amma wanda ya yi rõwa, kuma ya wadãtu da kansa. - Abubakar Gumi (Hausa)
92:9
وَكَذَّبَ بِٱلْحُسْنَىٰ
92:9
Kuma ya ƙaryatar da kalma mai kyãwo. - Abubakar Gumi (Hausa)
92:10
فَسَنُيَسِّرُهُۥ لِلْعُسْرَىٰ
92:10
To, zã Mu sauƙaƙke masa har ya kai ga tsanani. - Abubakar Gumi (Hausa)
92:11
وَمَا يُغْنِى عَنْهُ مَالُهُۥٓ إِذَا تَرَدَّىٰٓ
92:11
Kuma dũkiyarsa ba ta wadãtar masa da kõme ba, a lõkacin da ya gangara (a wuta). - Abubakar Gumi (Hausa)
92:12
إِنَّ عَلَيْنَا لَلْهُدَىٰ
92:12
Lãlle aikinMu ne, Mu bayyana shiriya. - Abubakar Gumi (Hausa)
92:13
وَإِنَّ لَنَا لَلْـَٔاخِرَةَ وَٱلْأُولَىٰ
92:13
Kuma lalle ne Lãhira da duniya Namu ne. - Abubakar Gumi (Hausa)
92:14
فَأَنذَرْتُكُمْ نَارًا تَلَظَّىٰ
92:14
Sabõda haka, Na yi maku gargaɗi da wuta mai babbaka. - Abubakar Gumi (Hausa)
92:15
لَا يَصْلَىٰهَآ إِلَّا ٱلْأَشْقَى
92:15
Bãbu mai shigarta sai mafi shaƙãwa. - Abubakar Gumi (Hausa)
92:16
ٱلَّذِى كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰ
92:16
Wanda ya ƙaryata, kuma ya jũya bãya. - Abubakar Gumi (Hausa)
92:17
وَسَيُجَنَّبُهَا ٱلْأَتْقَى
92:17
Kuma mafi taƙawa zai nisance ta. - Abubakar Gumi (Hausa)
92:18
ٱلَّذِى يُؤْتِى مَالَهُۥ يَتَزَكَّىٰ
92:18
Wanda yake bãyar da dũkiyarsa, alhãli yana tsarkaka. - Abubakar Gumi (Hausa)
92:19
وَمَا لِأَحَدٍ عِندَهُۥ مِن نِّعْمَةٍ تُجْزَىٰٓ
92:19
Alhãli bãbu wani mai wata ni'ima wurinsa wadda ake nẽman sakamakonta. - Abubakar Gumi (Hausa)
92:20
إِلَّا ٱبْتِغَآءَ وَجْهِ رَبِّهِ ٱلْأَعْلَىٰ
92:20
Fãce dai nẽman yardar Ubangijinsa Mafi ɗaukaka. - Abubakar Gumi (Hausa)
92:21
وَلَسَوْفَ يَرْضَىٰ
92:21
To, lalle ne zai yarda (da sakamakon da zã a bã shi). - Abubakar Gumi (Hausa)