Selected
                        Original Text
                        
                    
                
                    
                        Abubakar Gumi
                        
                        
                        
                    
                
                Abdullah Yusuf Ali
Abdul Majid Daryabadi
Abul Ala Maududi
Ahmed Ali
Ahmed Raza Khan
A. J. Arberry
Ali Quli Qarai
Hasan al-Fatih Qaribullah and Ahmad Darwish
Mohammad Habib Shakir
Mohammed Marmaduke William Pickthall
Muhammad Sarwar
Muhammad Taqi-ud-Din al-Hilali and Muhammad Muhsin Khan
Safi-ur-Rahman al-Mubarakpuri
Saheeh International
Talal Itani
Transliteration
Wahiduddin Khan
                    بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
                
                
                    In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.
                
            
                    84:1
                    إِذَا ٱلسَّمَآءُ ٱنشَقَّتْ
                
                
                
                
                
                    84:1
                    Idan sama ta kẽce,  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    84:2
                    وَأَذِنَتْ لِرَبِّهَا وَحُقَّتْ
                
                
                
                
                
                    84:2
                    Ta saurari Ubangijinta, kuma aka wajabta mata yin saurãron,  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    84:3
                    وَإِذَا ٱلْأَرْضُ مُدَّتْ
                
                
                
                
                
                    84:3
                    Kuma idan ƙasã aka mĩƙe ta,  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    84:4
                    وَأَلْقَتْ مَا فِيهَا وَتَخَلَّتْ
                
                
                
                
                
                    84:4
                    Kuma ta jẽfar da abin da yake a cikinta, tã wõfinta daga kõme.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    84:5
                    وَأَذِنَتْ لِرَبِّهَا وَحُقَّتْ
                
                
                
                
                
                    84:5
                    Kuma ta saurãri Ubangijinta, aka wajabta mata yin saurãren,  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    84:6
                    يَـٰٓأَيُّهَا ٱلْإِنسَـٰنُ إِنَّكَ كَادِحٌ إِلَىٰ رَبِّكَ كَدْحًا فَمُلَـٰقِيهِ
                
                
                
                
                
                    84:6
                    Ya kai mutum! Lalle ne kai mai aikin wahal da kai ne zuwa ga Ubangijinka, wahala mai tsanani, To, kai mai haɗuwa da Shi ne.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    84:7
                    فَأَمَّا مَنْ أُوتِىَ كِتَـٰبَهُۥ بِيَمِينِهِۦ
                
                
                
                
                
                    84:7
                    To, amma wanda aka bai wa littãfinsa da damansa.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    84:8
                    فَسَوْفَ يُحَاسَبُ حِسَابًا يَسِيرًا
                
                
                
                
                
                    84:8
                    To, za a yi masa hisãbi, hisãbi mai sauƙi.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    84:9
                    وَيَنقَلِبُ إِلَىٰٓ أَهْلِهِۦ مَسْرُورًا
                
                
                
                
                
                    84:9
                    Kuma ya jũya zuwa ga iyãlinsa (a cikin Aljanna), yanã mai raha.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    84:10
                    وَأَمَّا مَنْ أُوتِىَ كِتَـٰبَهُۥ وَرَآءَ ظَهْرِهِۦ
                
                
                
                
                
                    84:10
                    Kuma amma wanda aka bai wa littãfinsa, daga wajen bãyansa.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    84:11
                    فَسَوْفَ يَدْعُوا۟ ثُبُورًا
                
                
                
                
                
                    84:11
                    To, zã shi dinga kiran halaka!  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    84:12
                    وَيَصْلَىٰ سَعِيرًا
                
                
                
                
                
                    84:12
                    Kuma ya shiga sa'ĩr.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    84:13
                    إِنَّهُۥ كَانَ فِىٓ أَهْلِهِۦ مَسْرُورًا
                
                
                
                
                
                    84:13
                    Lal1e ne shi, yã kasance (a dũniya) cikin iyãlinsa yanã mai raha.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    84:14
                    إِنَّهُۥ ظَنَّ أَن لَّن يَحُورَ
                
                
                
                
                
                    84:14
                    Lalle ne yã yi zaton bã zai kõmo ba.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    84:15
                    بَلَىٰٓ إِنَّ رَبَّهُۥ كَانَ بِهِۦ بَصِيرًا
                
                
                
                
                
                    84:15
                    Na'am! Lalle ne, Ubangijinsa Ya kasance Mai gani gare shi.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    84:16
                    فَلَآ أُقْسِمُ بِٱلشَّفَقِ
                
                
                
                
                
                    84:16
                    To, ba sai Nã rantse da shafaƙi ba.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    84:17
                    وَٱلَّيْلِ وَمَا وَسَقَ
                
                
                
                
                
                    84:17
                    Da dare, da abin da ya ƙunsa.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    84:18
                    وَٱلْقَمَرِ إِذَا ٱتَّسَقَ
                
                
                
                
                
                    84:18
                    Da watã idan (haskensa) ya cika.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    84:19
                    لَتَرْكَبُنَّ طَبَقًا عَن طَبَقٍ
                
                
                
                
                
                    84:19
                    Lalle ne kunã hawan wani hãli daga wani hãli.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    84:20
                    فَمَا لَهُمْ لَا يُؤْمِنُونَ
                
                
                
                
                
                    84:20
                    To, mẽ ya sãme su, ba su yin ĩmãni?  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    84:21
                    وَإِذَا قُرِئَ عَلَيْهِمُ ٱلْقُرْءَانُ لَا يَسْجُدُونَ ۩
                
                
                
                
                
                    84:21
                    Kuma idan an karanta Alkur'ãni a kansu, bã su yin tawãli'u?  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    84:22
                    بَلِ ٱلَّذِينَ كَفَرُوا۟ يُكَذِّبُونَ
                
                
                
                
                
                    84:22
                    Ba haka ba! waɗanda suka kãfirta, sai ƙaryatãwa suke yi.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    84:23
                    وَٱللَّهُ أَعْلَمُ بِمَا يُوعُونَ
                
                
                
                
                
                    84:23
                    Alhãli Allah Shĩ ne Mafi sani ga abin a suke tãrãwa.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    84:24
                    فَبَشِّرْهُم بِعَذَابٍ أَلِيمٍ
                
                
                
                
                
                    84:24
                    Saboda haka, ka yi musu bushãra da azãba mai raɗaɗi.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    84:25
                    إِلَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ وَعَمِلُوا۟ ٱلصَّـٰلِحَـٰتِ لَهُمْ أَجْرٌ غَيْرُ مَمْنُونٍۭ
                
                
                
                
                
                    84:25
                    Fãce waɗanda suka yi ĩmãni, suka aikata ayyukan ƙwarai, sunã da wani sakamako wanda bã ya yankẽwa.  - Abubakar Gumi (Hausa)