Selected

Original Text
Abubakar Gumi

Available Translations

84 Al-'Inshiqāq ٱلْإِنْشِقَاق

< Previous   25 Āyah   The Sundering      Next >  

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.

84:1 إِذَا ٱلسَّمَآءُ ٱنشَقَّتْ
84:1
Abubakar Gumi (Hausa) :
Idan sama ta kẽce,

84:2 وَأَذِنَتْ لِرَبِّهَا وَحُقَّتْ
84:2
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ta saurari Ubangijinta, kuma aka wajabta mata yin saurãron,

84:3 وَإِذَا ٱلْأَرْضُ مُدَّتْ
84:3
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma idan ƙasã aka mĩƙe ta,

84:4 وَأَلْقَتْ مَا فِيهَا وَتَخَلَّتْ
84:4
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma ta jẽfar da abin da yake a cikinta, tã wõfinta daga kõme.

84:5 وَأَذِنَتْ لِرَبِّهَا وَحُقَّتْ
84:5
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma ta saurãri Ubangijinta, aka wajabta mata yin saurãren,

84:6 يَـٰٓأَيُّهَا ٱلْإِنسَـٰنُ إِنَّكَ كَادِحٌ إِلَىٰ رَبِّكَ كَدْحًا فَمُلَـٰقِيهِ
84:6
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ya kai mutum! Lalle ne kai mai aikin wahal da kai ne zuwa ga Ubangijinka, wahala mai tsanani, To, kai mai haɗuwa da Shi ne.

84:7 فَأَمَّا مَنْ أُوتِىَ كِتَـٰبَهُۥ بِيَمِينِهِۦ
84:7
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, amma wanda aka bai wa littãfinsa da damansa.

84:8 فَسَوْفَ يُحَاسَبُ حِسَابًا يَسِيرًا
84:8
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, za a yi masa hisãbi, hisãbi mai sauƙi.

84:9 وَيَنقَلِبُ إِلَىٰٓ أَهْلِهِۦ مَسْرُورًا
84:9
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma ya jũya zuwa ga iyãlinsa (a cikin Aljanna), yanã mai raha.

84:10 وَأَمَّا مَنْ أُوتِىَ كِتَـٰبَهُۥ وَرَآءَ ظَهْرِهِۦ
84:10
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma amma wanda aka bai wa littãfinsa, daga wajen bãyansa.

84:11 فَسَوْفَ يَدْعُوا۟ ثُبُورًا
84:11
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, zã shi dinga kiran halaka!

84:12 وَيَصْلَىٰ سَعِيرًا
84:12
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma ya shiga sa'ĩr.

84:13 إِنَّهُۥ كَانَ فِىٓ أَهْلِهِۦ مَسْرُورًا
84:13
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lal1e ne shi, yã kasance (a dũniya) cikin iyãlinsa yanã mai raha.

84:14 إِنَّهُۥ ظَنَّ أَن لَّن يَحُورَ
84:14
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne yã yi zaton bã zai kõmo ba.

84:15 بَلَىٰٓ إِنَّ رَبَّهُۥ كَانَ بِهِۦ بَصِيرًا
84:15
Abubakar Gumi (Hausa) :
Na'am! Lalle ne, Ubangijinsa Ya kasance Mai gani gare shi.

84:16 فَلَآ أُقْسِمُ بِٱلشَّفَقِ
84:16
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, ba sai Nã rantse da shafaƙi ba.

84:17 وَٱلَّيْلِ وَمَا وَسَقَ
84:17
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da dare, da abin da ya ƙunsa.

84:18 وَٱلْقَمَرِ إِذَا ٱتَّسَقَ
84:18
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da watã idan (haskensa) ya cika.

84:19 لَتَرْكَبُنَّ طَبَقًا عَن طَبَقٍ
84:19
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne kunã hawan wani hãli daga wani hãli.

84:20 فَمَا لَهُمْ لَا يُؤْمِنُونَ
84:20
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, mẽ ya sãme su, ba su yin ĩmãni?

84:21 وَإِذَا قُرِئَ عَلَيْهِمُ ٱلْقُرْءَانُ لَا يَسْجُدُونَ ۩
84:21
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma idan an karanta Alkur'ãni a kansu, bã su yin tawãli'u?

84:22 بَلِ ٱلَّذِينَ كَفَرُوا۟ يُكَذِّبُونَ
84:22
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ba haka ba! waɗanda suka kãfirta, sai ƙaryatãwa suke yi.

84:23 وَٱللَّهُ أَعْلَمُ بِمَا يُوعُونَ
84:23
Abubakar Gumi (Hausa) :
Alhãli Allah Shĩ ne Mafi sani ga abin a suke tãrãwa.

84:24 فَبَشِّرْهُم بِعَذَابٍ أَلِيمٍ
84:24
Abubakar Gumi (Hausa) :
Saboda haka, ka yi musu bushãra da azãba mai raɗaɗi.

84:25 إِلَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوا۟ وَعَمِلُوا۟ ٱلصَّـٰلِحَـٰتِ لَهُمْ أَجْرٌ غَيْرُ مَمْنُونٍۭ
84:25
Abubakar Gumi (Hausa) :
Fãce waɗanda suka yi ĩmãni, suka aikata ayyukan ƙwarai, sunã da wani sakamako wanda bã ya yankẽwa.