Selected
Original Text
Abubakar Gumi
Abdullah Yusuf Ali
Abdul Majid Daryabadi
Abul Ala Maududi
Ahmed Ali
Ahmed Raza Khan
A. J. Arberry
Ali Quli Qarai
Hasan al-Fatih Qaribullah and Ahmad Darwish
Mohammad Habib Shakir
Mohammed Marmaduke William Pickthall
Muhammad Sarwar
Muhammad Taqi-ud-Din al-Hilali and Muhammad Muhsin Khan
Safi-ur-Rahman al-Mubarakpuri
Saheeh International
Talal Itani
Transliteration
Wahiduddin Khan
بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.
91:1
وَٱلشَّمْسِ وَضُحَىٰهَا
91:1
Ina rantsuwa da rãnã da hantsinta. - Abubakar Gumi (Hausa)
91:2
وَٱلْقَمَرِ إِذَا تَلَىٰهَا
91:2
Kuma da wata idan ya bi ta. - Abubakar Gumi (Hausa)
91:3
وَٱلنَّهَارِ إِذَا جَلَّىٰهَا
91:3
Da yini a lõkacin da ya bayyana ta. - Abubakar Gumi (Hausa)
91:4
وَٱلَّيْلِ إِذَا يَغْشَىٰهَا
91:4
Da dare a lõkacin da ya ke rufe ta. - Abubakar Gumi (Hausa)
91:5
وَٱلسَّمَآءِ وَمَا بَنَىٰهَا
91:5
Da sama da abin da ya gina ta. - Abubakar Gumi (Hausa)
91:6
وَٱلْأَرْضِ وَمَا طَحَىٰهَا
91:6
Da ƙasã da abin da ya shimfiɗa ta. - Abubakar Gumi (Hausa)
91:7
وَنَفْسٍ وَمَا سَوَّىٰهَا
91:7
Da rai da abin da ya daidaita shi. - Abubakar Gumi (Hausa)
91:8
فَأَلْهَمَهَا فُجُورَهَا وَتَقْوَىٰهَا
91:8
Sa'an nan ya sanar da shi fãjircinsa da shiryuwarsa. - Abubakar Gumi (Hausa)
91:9
قَدْ أَفْلَحَ مَن زَكَّىٰهَا
91:9
Lalle ne wanda ya tsarkake shi (rai) ya sãmi babban rabo. - Abubakar Gumi (Hausa)
91:10
وَقَدْ خَابَ مَن دَسَّىٰهَا
91:10
Kuma lalle ne wanda ya turbuɗe shi (da laifi) ya tãɓe. - Abubakar Gumi (Hausa)
91:11
كَذَّبَتْ ثَمُودُ بِطَغْوَىٰهَآ
91:11
Samũdãwa sun ƙaryata (Annabinsu), dõmin girman kansu. - Abubakar Gumi (Hausa)
91:12
إِذِ ٱنۢبَعَثَ أَشْقَىٰهَا
91:12
A lõkacin da mafi shaƙãwarsu ya tafi (wurin sõke rãkumar sãlihu). - Abubakar Gumi (Hausa)
91:13
فَقَالَ لَهُمْ رَسُولُ ٱللَّهِ نَاقَةَ ٱللَّهِ وَسُقْيَـٰهَا
91:13
Sai Manzon Allah ya gaya musu cewa: "Ina tsõratar da ku ga rãƙumar Allah da ruwan shanta!" - Abubakar Gumi (Hausa)
91:14
فَكَذَّبُوهُ فَعَقَرُوهَا فَدَمْدَمَ عَلَيْهِمْ رَبُّهُم بِذَنۢبِهِمْ فَسَوَّىٰهَا
91:14
Sai suka ƙaryata shi, sa'an nan suka sõke ta. Sabõda haka Ubangijinsu Ya darkãke su, sabõda zunubinsu. Sa'an nan Ya daidaita ta (azãbar ga mai laifi da maras laifi). - Abubakar Gumi (Hausa)
91:15
وَلَا يَخَافُ عُقْبَـٰهَا
91:15
Kuma bã ya tsõron ãƙibarta (ita halakãwar). - Abubakar Gumi (Hausa)