Selected

Original Text
Abubakar Gumi

Available Translations

1 Al-Fātiĥah ٱلْفَاتِحَة

7 Āyah   The Opener      Next >  

1:1 بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَـٰنِ ٱلرَّحِيمِ
1:1
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai.

1:2 ٱلْحَمْدُ لِلَّهِ رَبِّ ٱلْعَـٰلَمِينَ
1:2
Abubakar Gumi (Hausa) :
Godiya ta tabbata ga Allah, Ubangijin halittu;

1:3 ٱلرَّحْمَـٰنِ ٱلرَّحِيمِ
1:3
Abubakar Gumi (Hausa) :
Mai rahama, Mai jin ƙai;

1:4 مَـٰلِكِ يَوْمِ ٱلدِّينِ
1:4
Abubakar Gumi (Hausa) :
Mai nuna Mulkin Rãnar Sakamako.

1:5 إِيَّاكَ نَعْبُدُ وَإِيَّاكَ نَسْتَعِينُ
1:5
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kai muke bauta wa, kuma Kai muke neman taimakonKa.

1:6 ٱهْدِنَا ٱلصِّرَٰطَ ٱلْمُسْتَقِيمَ
1:6
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ka shiryar da mu ga hanya madaidaiciya.

1:7 صِرَٰطَ ٱلَّذِينَ أَنْعَمْتَ عَلَيْهِمْ غَيْرِ ٱلْمَغْضُوبِ عَلَيْهِمْ وَلَا ٱلضَّآلِّينَ
1:7
Abubakar Gumi (Hausa) :
Hanyar waɗanda Ka yi wa ni'ima, ba waɗanda aka yi wa fushi ba, kuma ba ɓatattu ba.