Selected

Original Text
Abubakar Gumi

Available Translations

87 Al-'A`lá ٱلْأَعْلَىٰ

< Previous   19 Āyah   The Most High      Next >  

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.

87:1 سَبِّحِ ٱسْمَ رَبِّكَ ٱلْأَعْلَى
87:1
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ka tsarkake sũnan Ubangijinka Mafi ɗaukaka.

87:2 ٱلَّذِى خَلَقَ فَسَوَّىٰ
87:2
Abubakar Gumi (Hausa) :
Wanda Yã yi halitta sa'an nan Ya daidaita abin halittar.

87:3 وَٱلَّذِى قَدَّرَ فَهَدَىٰ
87:3
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma Wanda Ya ƙaddara (abin da Ya so) sannan Ya shiryar, (da mutum ga hanyar alhẽri da ta sharri).

87:4 وَٱلَّذِىٓ أَخْرَجَ ٱلْمَرْعَىٰ
87:4
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma Wanda Ya fitar da makiyãyã.

87:5 فَجَعَلَهُۥ غُثَآءً أَحْوَىٰ
87:5
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan Ya mayar da ita ƙeƙasassa, baƙa.

87:6 سَنُقْرِئُكَ فَلَا تَنسَىٰٓ
87:6
Abubakar Gumi (Hausa) :
Za mu karantar da kai (Alƙur'ãni) sabõda haka bã zã ka mantã (shi) ba.

87:7 إِلَّا مَا شَآءَ ٱللَّهُ ۚ إِنَّهُۥ يَعْلَمُ ٱلْجَهْرَ وَمَا يَخْفَىٰ
87:7
Abubakar Gumi (Hausa) :
Fãce abin da Allah Ya so, lalle ne Shi (Allah) Ya san bayyane da abin da yake bõye.

87:8 وَنُيَسِّرُكَ لِلْيُسْرَىٰ
87:8
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma za Mu sauƙaƙe maka (al'amari) zuwa ga (Shari'a) mai sauƙi.

87:9 فَذَكِّرْ إِن نَّفَعَتِ ٱلذِّكْرَىٰ
87:9
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sabõda baka, ka tunãtar, idan tunatarwa zã ta yi amfãni.

87:10 سَيَذَّكَّرُ مَن يَخْشَىٰ
87:10
Abubakar Gumi (Hausa) :
Wanda yake tsõron (Allah) Zai tuna.

87:11 وَيَتَجَنَّبُهَا ٱلْأَشْقَى
87:11
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma shaƙiyyi, zai nisanceta,

87:12 ٱلَّذِى يَصْلَى ٱلنَّارَ ٱلْكُبْرَىٰ
87:12
Abubakar Gumi (Hausa) :
Wanda zai shiga wutar da tã fi girma.

87:13 ثُمَّ لَا يَمُوتُ فِيهَا وَلَا يَحْيَىٰ
87:13
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan bã zai mutu ba a cikinta, kuma bã zai rãyu ba.

87:14 قَدْ أَفْلَحَ مَن تَزَكَّىٰ
87:14
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne wanda ya tsarkaka (da ĩmãni) yã sãmu babban rabo.

87:15 وَذَكَرَ ٱسْمَ رَبِّهِۦ فَصَلَّىٰ
87:15
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma ya ambaci sũnan Ubangijinsa, sa'an nan yã yi salla.

87:16 بَلْ تُؤْثِرُونَ ٱلْحَيَوٰةَ ٱلدُّنْيَا
87:16
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ba haka ba! Kunã zãɓin rãyuwa ta kusa dũniya.

87:17 وَٱلْـَٔاخِرَةُ خَيْرٌ وَأَبْقَىٰٓ
87:17
Abubakar Gumi (Hausa) :
Alhãli Lãhira ita ce mafi alheri kuma mafi wanzuwa.

87:18 إِنَّ هَـٰذَا لَفِى ٱلصُّحُفِ ٱلْأُولَىٰ
87:18
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne, wannan yanã a cikin littafan farko.

87:19 صُحُفِ إِبْرَٰهِيمَ وَمُوسَىٰ
87:19
Abubakar Gumi (Hausa) :
Littaffan Ibrãhĩm da Mũsã.