Selected

Original Text
Abubakar Gumi

Available Translations

70 Al-Ma`ārij ٱلْمَعَارِج

< Previous   44 Āyah   The Ascending Stairways      Next >  

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.

70:1 سَأَلَ سَآئِلٌۢ بِعَذَابٍ وَاقِعٍ
70:1
Abubakar Gumi (Hausa) :
Wani mai tambaya yã yi tambaya game da azãba, mai aukuwa.

70:2 لِّلْكَـٰفِرِينَ لَيْسَ لَهُۥ دَافِعٌ
70:2
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ga kãfirai, bã ta da mai tunkuɗẽwa.

70:3 مِّنَ ٱللَّهِ ذِى ٱلْمَعَارِجِ
70:3
Abubakar Gumi (Hausa) :
Daga Allah Mai matãkala.

70:4 تَعْرُجُ ٱلْمَلَـٰٓئِكَةُ وَٱلرُّوحُ إِلَيْهِ فِى يَوْمٍ كَانَ مِقْدَارُهُۥ خَمْسِينَ أَلْفَ سَنَةٍ
70:4
Abubakar Gumi (Hausa) :
Malã'iku da Ruhi (Jibrila) sunã tãkãwa zuwa gare Shi, a cikin yini wanda gwargwadonsa, shẽkara dubu hamsin ne.

70:5 فَٱصْبِرْ صَبْرًا جَمِيلًا
70:5
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sabõda haka, ka yi haƙuri, haƙuri mai kyãwo.

70:6 إِنَّهُمْ يَرَوْنَهُۥ بَعِيدًا
70:6
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne su, sunã ganin ta mai nĩsa.

70:7 وَنَرَىٰهُ قَرِيبًا
70:7
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma Mu, Muna ganin ta a kusa.

70:8 يَوْمَ تَكُونُ ٱلسَّمَآءُ كَٱلْمُهْلِ
70:8
Abubakar Gumi (Hausa) :
Rãnar da sama zã ta kasance kamar narkakkar azurfa.

70:9 وَتَكُونُ ٱلْجِبَالُ كَٱلْعِهْنِ
70:9
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma duwãtsu su zama kamar saɓin sũfi.

70:10 وَلَا يَسْـَٔلُ حَمِيمٌ حَمِيمًا
70:10
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma abõki bã ya tambayar inda wani abõki yake.

70:11 يُبَصَّرُونَهُمْ ۚ يَوَدُّ ٱلْمُجْرِمُ لَوْ يَفْتَدِى مِنْ عَذَابِ يَوْمِئِذٍۭ بِبَنِيهِ
70:11
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ana sanya su, su gajũna, mai laifi na gũrin dã zai iya yin fansa, daga azãbar rãnar nan, da ɗiyansa,

70:12 وَصَـٰحِبَتِهِۦ وَأَخِيهِ
70:12
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da matarsa da ɗan'uwansa.

70:13 وَفَصِيلَتِهِ ٱلَّتِى تُـْٔوِيهِ
70:13
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da danginsa, mãsu tattarã shi.

70:14 وَمَن فِى ٱلْأَرْضِ جَمِيعًا ثُمَّ يُنجِيهِ
70:14
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da wanda ke a cikin dũniya duka gabã ɗaya, sa'an nan fansar, ta tsĩrar da shi.

70:15 كَلَّآ ۖ إِنَّهَا لَظَىٰ
70:15
Abubakar Gumi (Hausa) :
A'aha! Lalle ne fa, ita ce Lazã,

70:16 نَزَّاعَةً لِّلشَّوَىٰ
70:16
Abubakar Gumi (Hausa) :
Mai twãle fãtar goshi.

70:17 تَدْعُوا۟ مَنْ أَدْبَرَ وَتَوَلَّىٰ
70:17
Abubakar Gumi (Hausa) :
Tanã kiran wanda ya jũya bãya (daga addini) kuma ya kau da kai.

70:18 وَجَمَعَ فَأَوْعَىٰٓ
70:18
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ya tãra (dũkiya), kuma ya sanya ta a cikin jaka.

70:19 ۞ إِنَّ ٱلْإِنسَـٰنَ خُلِقَ هَلُوعًا
70:19
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne mutum an halitta shi mai ciwon kwaɗayi.

70:20 إِذَا مَسَّهُ ٱلشَّرُّ جَزُوعًا
70:20
Abubakar Gumi (Hausa) :
Idan sharri ya shãfe shi, ya kãsa haƙuri.

70:21 وَإِذَا مَسَّهُ ٱلْخَيْرُ مَنُوعًا
70:21
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma idan alhẽri ya shãfe shi, ya yi rõwa.

70:22 إِلَّا ٱلْمُصَلِّينَ
70:22
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai mãsu yin salla,

70:23 ٱلَّذِينَ هُمْ عَلَىٰ صَلَاتِهِمْ دَآئِمُونَ
70:23
Abubakar Gumi (Hausa) :
Waɗanda suke, a kan sallarsu, su, mãsu dawwama ne.

70:24 وَٱلَّذِينَ فِىٓ أَمْوَٰلِهِمْ حَقٌّ مَّعْلُومٌ
70:24
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma waɗanda a cikin dũkiyarsu, akwai wani haƙƙi sananne.

70:25 لِّلسَّآئِلِ وَٱلْمَحْرُومِ
70:25
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ga (matalauci) mai rõƙo da wanda aka hanã wa roƙon.

70:26 وَٱلَّذِينَ يُصَدِّقُونَ بِيَوْمِ ٱلدِّينِ
70:26
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da waɗannan da ke gaskata rãnar sakamako.

70:27 وَٱلَّذِينَ هُم مِّنْ عَذَابِ رَبِّهِم مُّشْفِقُونَ
70:27
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da waɗannan sabõda azãbar Ubangijinsu, suna jin tsõro.

70:28 إِنَّ عَذَابَ رَبِّهِمْ غَيْرُ مَأْمُونٍ
70:28
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne, azãbar Ubangijinsu bã wadda ake iya amincẽwaba ce.

70:29 وَٱلَّذِينَ هُمْ لِفُرُوجِهِمْ حَـٰفِظُونَ
70:29
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da waɗanda suke, ga farjojinsu, mãsu tsarewa ne.

70:30 إِلَّا عَلَىٰٓ أَزْوَٰجِهِمْ أَوْ مَا مَلَكَتْ أَيْمَـٰنُهُمْ فَإِنَّهُمْ غَيْرُ مَلُومِينَ
70:30
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai fa a kan matan aurensu da abin da hannayensu na dãma suka mallaka. To lalle ne sũkam ba waɗanda ake zargi ba ne.

70:31 فَمَنِ ٱبْتَغَىٰ وَرَآءَ ذَٰلِكَ فَأُو۟لَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلْعَادُونَ
70:31
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, duk wanda ya nẽmi abin da yake a bayan wannan, to, waɗancan sũ ne mãsu ƙetare iyãka.

70:32 وَٱلَّذِينَ هُمْ لِأَمَـٰنَـٰتِهِمْ وَعَهْدِهِمْ رَٰعُونَ
70:32
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma da waɗannan da suke ga amãnõninsu da alkawarinsu mãsu tsarẽwa ne.

70:33 وَٱلَّذِينَ هُم بِشَهَـٰدَٰتِهِمْ قَآئِمُونَ
70:33
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma da waɗanda suke, ga shaidarsu, mãsu dãgẽwa ne.

70:34 وَٱلَّذِينَ هُمْ عَلَىٰ صَلَاتِهِمْ يُحَافِظُونَ
70:34
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma waɗanda suke, a kan sallarsu, mãsu tsarẽwa ne.

70:35 أُو۟لَـٰٓئِكَ فِى جَنَّـٰتٍ مُّكْرَمُونَ
70:35
Abubakar Gumi (Hausa) :
Waɗannan, a cikin gidãjen Aljanna, waɗanda ake girmamãwa ne

70:36 فَمَالِ ٱلَّذِينَ كَفَرُوا۟ قِبَلَكَ مُهْطِعِينَ
70:36
Abubakar Gumi (Hausa) :
Mẽ yã sãmi waɗanda suka kãfirta, a wajenka, sunã gaugãwar (gudu).

70:37 عَنِ ٱلْيَمِينِ وَعَنِ ٱلشِّمَالِ عِزِينَ
70:37
Abubakar Gumi (Hausa) :
Daga jihar dãma, kuma daga jihar hagu, jama'a-jama'a!

70:38 أَيَطْمَعُ كُلُّ ٱمْرِئٍ مِّنْهُمْ أَن يُدْخَلَ جَنَّةَ نَعِيمٍ
70:38
Abubakar Gumi (Hausa) :
Shin kõwane mutum daga cikinsu yana nẽman a shigar da shi a Aljannar ni'ima ne (ba da wani aiki ba)?

70:39 كَلَّآ ۖ إِنَّا خَلَقْنَـٰهُم مِّمَّا يَعْلَمُونَ
70:39
Abubakar Gumi (Hausa) :
A'aha! Lalle Mũ, Mun halitta su, daga abin da suka sani.

70:40 فَلَآ أُقْسِمُ بِرَبِّ ٱلْمَشَـٰرِقِ وَٱلْمَغَـٰرِبِ إِنَّا لَقَـٰدِرُونَ
70:40
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sabõda haka ba sai Na yi rantsuwa da Ubangijin wurãren ɓullõwar rãna da wurãren fãɗuwarta ba, lalle Mũ, Mãsu iyãwa ne.

70:41 عَلَىٰٓ أَن نُّبَدِّلَ خَيْرًا مِّنْهُمْ وَمَا نَحْنُ بِمَسْبُوقِينَ
70:41
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ga Mu musanya waɗanda suke mafi alhẽri, daga gare su. Kuma ba Mu kasance waɗanda ake rinjãya ba.

70:42 فَذَرْهُمْ يَخُوضُوا۟ وَيَلْعَبُوا۟ حَتَّىٰ يُلَـٰقُوا۟ يَوْمَهُمُ ٱلَّذِى يُوعَدُونَ
70:42
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sabõda haka ka bar su, su dulmuya, kuma su yi wãsã, har su haɗu da rãnarsu wadda ake yi musu alkawari (da ita).

70:43 يَوْمَ يَخْرُجُونَ مِنَ ٱلْأَجْدَاثِ سِرَاعًا كَأَنَّهُمْ إِلَىٰ نُصُبٍ يُوفِضُونَ
70:43
Abubakar Gumi (Hausa) :
Rãnar da suke fitowa daga kaburbura da gaugãwa, kamar sũ, zuwa ga wata kafaffiyar (tuta), suke yin gaugãwa.

70:44 خَـٰشِعَةً أَبْصَـٰرُهُمْ تَرْهَقُهُمْ ذِلَّةٌ ۚ ذَٰلِكَ ٱلْيَوْمُ ٱلَّذِى كَانُوا۟ يُوعَدُونَ
70:44
Abubakar Gumi (Hausa) :
Maƙaskanta ga idanunsu, wani walakanci yana rufe su. wannan shi ne yinin da suka kasance ana yi musa alkawari (a kansa.)