Selected
Original Text
Abubakar Gumi
Abdullah Yusuf Ali
Abdul Majid Daryabadi
Abul Ala Maududi
Ahmed Ali
Ahmed Raza Khan
A. J. Arberry
Ali Quli Qarai
Hasan al-Fatih Qaribullah and Ahmad Darwish
Mohammad Habib Shakir
Mohammed Marmaduke William Pickthall
Muhammad Sarwar
Muhammad Taqi-ud-Din al-Hilali and Muhammad Muhsin Khan
Safi-ur-Rahman al-Mubarakpuri
Saheeh International
Talal Itani
Transliteration
Wahiduddin Khan
بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.
82:1
إِذَا ٱلسَّمَآءُ ٱنفَطَرَتْ
82:1
Idan sama ta tsãge. - Abubakar Gumi (Hausa)
82:2
وَإِذَا ٱلْكَوَاكِبُ ٱنتَثَرَتْ
82:2
Kuma idan taurãri suka wãtse. - Abubakar Gumi (Hausa)
82:3
وَإِذَا ٱلْبِحَارُ فُجِّرَتْ
82:3
Kuma idan tẽkuna aka facce su. - Abubakar Gumi (Hausa)
82:4
وَإِذَا ٱلْقُبُورُ بُعْثِرَتْ
82:4
Kuma idan kaburbura aka tõne su. - Abubakar Gumi (Hausa)
82:5
عَلِمَتْ نَفْسٌ مَّا قَدَّمَتْ وَأَخَّرَتْ
82:5
Rai yã san abin da ya gabatar, da abin da yã jinkirtar. - Abubakar Gumi (Hausa)
82:6
يَـٰٓأَيُّهَا ٱلْإِنسَـٰنُ مَا غَرَّكَ بِرَبِّكَ ٱلْكَرِيمِ
82:6
Yã kai mutum! Mẽ ya rũɗe ka game da Ubangijinka, Mai karimci. - Abubakar Gumi (Hausa)
82:7
ٱلَّذِى خَلَقَكَ فَسَوَّىٰكَ فَعَدَلَكَ
82:7
Wanda Ya halitta ka sa'an nan ya daidaitã ka, Ya kuma tsakaitã ka. - Abubakar Gumi (Hausa)
82:8
فِىٓ أَىِّ صُورَةٍ مَّا شَآءَ رَكَّبَكَ
82:8
A cikin kõwace irin sũra Ya so Ya ginã ka a kanta. - Abubakar Gumi (Hausa)
82:9
كَلَّا بَلْ تُكَذِّبُونَ بِٱلدِّينِ
82:9
A'aha, bã haka ba, kuna ƙaryatãwa game da sakamako! - Abubakar Gumi (Hausa)
82:10
وَإِنَّ عَلَيْكُمْ لَحَـٰفِظِينَ
82:10
Lalle ne, a kanku, haƙiƙa akwai matsara. - Abubakar Gumi (Hausa)
82:11
كِرَامًا كَـٰتِبِينَ
82:11
Mãsu daraja, marubũta. - Abubakar Gumi (Hausa)
82:12
يَعْلَمُونَ مَا تَفْعَلُونَ
82:12
Sunã sanin abin da kuke aikatãwa. - Abubakar Gumi (Hausa)
82:13
إِنَّ ٱلْأَبْرَارَ لَفِى نَعِيمٍ
82:13
Lalle ne, mãsu ɗã'ã ga Allah, dãhir, suna cikin ni'ima. - Abubakar Gumi (Hausa)
82:14
وَإِنَّ ٱلْفُجَّارَ لَفِى جَحِيمٍ
82:14
Kuma lalle ne, fãjirai, dãhir, sunã cikin Jahĩm. - Abubakar Gumi (Hausa)
82:15
يَصْلَوْنَهَا يَوْمَ ٱلدِّينِ
82:15
Zã su shigẽ ta a rãnar sakamako. - Abubakar Gumi (Hausa)
82:16
وَمَا هُمْ عَنْهَا بِغَآئِبِينَ
82:16
Bã zã su faku daga gare ta ba. - Abubakar Gumi (Hausa)
82:17
وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا يَوْمُ ٱلدِّينِ
82:17
Kuma mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽ wa rẽnar sakamako? - Abubakar Gumi (Hausa)
82:18
ثُمَّ مَآ أَدْرَىٰكَ مَا يَوْمُ ٱلدِّينِ
82:18
Sa'an nan, mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽ wa rãnar sakamako? - Abubakar Gumi (Hausa)
82:19
يَوْمَ لَا تَمْلِكُ نَفْسٌ لِّنَفْسٍ شَيْـًٔا ۖ وَٱلْأَمْرُ يَوْمَئِذٍ لِّلَّهِ
82:19
Rãnã ce da wani rai ba ya iya mallakar kõme dõmin wani rai al'amari, a rãnar nan, ga Allah (ɗai) yake. - Abubakar Gumi (Hausa)