Selected
                        Original Text
                        
                    
                
                    
                        Abubakar Gumi
                        
                        
                        
                    
                
                Abdullah Yusuf Ali
Abdul Majid Daryabadi
Abul Ala Maududi
Ahmed Ali
Ahmed Raza Khan
A. J. Arberry
Ali Quli Qarai
Hasan al-Fatih Qaribullah and Ahmad Darwish
Mohammad Habib Shakir
Mohammed Marmaduke William Pickthall
Muhammad Sarwar
Muhammad Taqi-ud-Din al-Hilali and Muhammad Muhsin Khan
Safi-ur-Rahman al-Mubarakpuri
Saheeh International
Talal Itani
Transliteration
Wahiduddin Khan
                    بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
                
                
                    In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.
                
            
                    79:1
                    وَٱلنَّـٰزِعَـٰتِ غَرْقًا
                
                
                
                
                
                    79:1
                    Ina rantsuwa da mala'iku mãsu fisgar rãyuka (na kafirai) da ƙarfi.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:2
                    وَٱلنَّـٰشِطَـٰتِ نَشْطًا
                
                
                
                
                
                    79:2
                    Da mãsu ɗibar rãyuka (na mũminai) da sauƙi a cikin nishãɗi.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:3
                    وَٱلسَّـٰبِحَـٰتِ سَبْحًا
                
                
                
                
                
                    79:3
                    Da mãsu sauka daga sama da umurnin Allah kamar suna iyo.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:4
                    فَٱلسَّـٰبِقَـٰتِ سَبْقًا
                
                
                
                
                
                    79:4
                    Sa'an nan, su zama mãsu gaugãwa (da umurnin Allah) kamar suna tsẽre.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:5
                    فَٱلْمُدَبِّرَٰتِ أَمْرًا
                
                
                
                
                
                    79:5
                    Sa, an nan, su kasance masu shirya gudanar da umurni.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:6
                    يَوْمَ تَرْجُفُ ٱلرَّاجِفَةُ
                
                
                
                
                
                    79:6
                    Rãnar da mai girgiza abũbuwa (bũsar farko) zã ta kaɗa.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:7
                    تَتْبَعُهَا ٱلرَّادِفَةُ
                
                
                
                
                
                    79:7
                    Mai biyar ta (bũsa ta biyu) nã biye.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:8
                    قُلُوبٌ يَوْمَئِذٍ وَاجِفَةٌ
                
                
                
                
                
                    79:8
                    Wasu zukãta, a rãnar nan, mãsu jin tsõro ne.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:9
                    أَبْصَـٰرُهَا خَـٰشِعَةٌ
                
                
                
                
                
                    79:9
                    Alhãli idãnunsu na ƙasƙantattu.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:10
                    يَقُولُونَ أَءِنَّا لَمَرْدُودُونَ فِى ٱلْحَافِرَةِ
                
                
                
                
                
                    79:10
                    Sunã cẽwa "Ashe lalle zã a iya mayar da mu a kan sãwunmu?  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:11
                    أَءِذَا كُنَّا عِظَـٰمًا نَّخِرَةً
                
                
                
                
                
                    79:11
                    "Ashe, idan muka zama ƙasusuwa rududdugaggu?"  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:12
                    قَالُوا۟ تِلْكَ إِذًا كَرَّةٌ خَاسِرَةٌ
                
                
                
                
                
                    79:12
                    Suka ce: "Waccan kam kõmãwa ce, tãɓaɓɓiya!"  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:13
                    فَإِنَّمَا هِىَ زَجْرَةٌ وَٰحِدَةٌ
                
                
                
                
                
                    79:13
                    To, ita kam, tsãwa guda kawai ce.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:14
                    فَإِذَا هُم بِٱلسَّاهِرَةِ
                
                
                
                
                
                    79:14
                    Sai kawai gã su a bãyan ƙasa.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:15
                    هَلْ أَتَىٰكَ حَدِيثُ مُوسَىٰٓ
                
                
                
                
                
                    79:15
                    Shin, lãbãrin Mũsã ya zo maka?  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:16
                    إِذْ نَادَىٰهُ رَبُّهُۥ بِٱلْوَادِ ٱلْمُقَدَّسِ طُوًى
                
                
                
                
                
                    79:16
                    A lõkacin da Ubangijinsa Ya kirãye shi, a cikin kwari mai tsarki, wato Duwã?  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:17
                    ٱذْهَبْ إِلَىٰ فِرْعَوْنَ إِنَّهُۥ طَغَىٰ
                
                
                
                
                
                    79:17
                    Ka tafi zuwa ga Fir'auna, lalle ne shi, ya ƙẽtare haddi.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:18
                    فَقُلْ هَل لَّكَ إِلَىٰٓ أَن تَزَكَّىٰ
                
                
                
                
                
                    79:18
                    "Sai ka ce masa, Kõ zã ka so ka tsarkaka.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:19
                    وَأَهْدِيَكَ إِلَىٰ رَبِّكَ فَتَخْشَىٰ
                
                
                
                
                
                    79:19
                    "Kuma in shiryar da kai zuwa ga Ubangijinka domin ka ji tsoronSa?"  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:20
                    فَأَرَىٰهُ ٱلْـَٔايَةَ ٱلْكُبْرَىٰ
                
                
                
                
                
                    79:20
                    Sai ya nũna masa ãyar nan mafi girma.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:21
                    فَكَذَّبَ وَعَصَىٰ
                
                
                
                
                
                    79:21
                    Sai ya ƙaryata, kuma ya sãɓa (umurni),  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:22
                    ثُمَّ أَدْبَرَ يَسْعَىٰ
                
                
                
                
                
                    79:22
                    Sa'an nan ya jũya bãya, yanã tafiya da sauri.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:23
                    فَحَشَرَ فَنَادَىٰ
                
                
                
                
                
                    79:23
                    Sai ya yi gayya, sa'an nan ya yi kira.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:24
                    فَقَالَ أَنَا۠ رَبُّكُمُ ٱلْأَعْلَىٰ
                
                
                
                
                
                    79:24
                    Sai ya ce: "Nĩ ne Ubangijinku mafi ɗaudaka."  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:25
                    فَأَخَذَهُ ٱللَّهُ نَكَالَ ٱلْـَٔاخِرَةِ وَٱلْأُولَىٰٓ
                
                
                
                
                
                    79:25
                    Sabõda haka Allah Ya kama shi, dõmin azãbar maganar ƙarshe da ta farko.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:26
                    إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَعِبْرَةً لِّمَن يَخْشَىٰٓ
                
                
                
                
                
                    79:26
                    Lalle ne, a cikin wannan haƙiƙa akwai abin kula ga wanda yake tsõron Allah.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:27
                    ءَأَنتُمْ أَشَدُّ خَلْقًا أَمِ ٱلسَّمَآءُ ۚ بَنَىٰهَا
                
                
                
                
                
                    79:27
                    Shin, kũ ne mafi wuyar halitta ko sama? Allah Ya gina ta.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:28
                    رَفَعَ سَمْكَهَا فَسَوَّىٰهَا
                
                
                
                
                
                    79:28
                    Ya ɗaukaka rufinta, sa'an nan Ya daidaita ta.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:29
                    وَأَغْطَشَ لَيْلَهَا وَأَخْرَجَ ضُحَىٰهَا
                
                
                
                
                
                    79:29
                    Kuma Ya duhuntar da darenta, kuma Ya fitar da hantsinta.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:30
                    وَٱلْأَرْضَ بَعْدَ ذَٰلِكَ دَحَىٰهَآ
                
                
                
                
                
                    79:30
                    Kuma, ƙasa a bayan haka Ya mulmula ta.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:31
                    أَخْرَجَ مِنْهَا مَآءَهَا وَمَرْعَىٰهَا
                
                
                
                
                
                    79:31
                    Ya fitar da ruwanta daga gare ta da makiyãyarta.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:32
                    وَٱلْجِبَالَ أَرْسَىٰهَا
                
                
                
                
                
                    79:32
                    Da duwatsu, Yã kafe ta.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:33
                    مَتَـٰعًا لَّكُمْ وَلِأَنْعَـٰمِكُمْ
                
                
                
                
                
                    79:33
                    Domin jiyarwa dãɗi a gare ku, kuma ga dabbõbinku.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:34
                    فَإِذَا جَآءَتِ ٱلطَّآمَّةُ ٱلْكُبْرَىٰ
                
                
                
                
                
                    79:34
                    To, idan uwar masĩfu, mafi girma, ta zo.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:35
                    يَوْمَ يَتَذَكَّرُ ٱلْإِنسَـٰنُ مَا سَعَىٰ
                
                
                
                
                
                    79:35
                    Rãnar da mutum zai yi tunãnin abin da ya aikata.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:36
                    وَبُرِّزَتِ ٱلْجَحِيمُ لِمَن يَرَىٰ
                
                
                
                
                
                    79:36
                    Kuma, a bayyana Jahĩm ga mai gani.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:37
                    فَأَمَّا مَن طَغَىٰ
                
                
                
                
                
                    79:37
                    To, amma wanda ya yi girman kai.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:38
                    وَءَاثَرَ ٱلْحَيَوٰةَ ٱلدُّنْيَا
                
                
                
                
                
                    79:38
                    Kuma, ya zãɓi rãyuwa ta kusa, (wato dũniya).  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:39
                    فَإِنَّ ٱلْجَحِيمَ هِىَ ٱلْمَأْوَىٰ
                
                
                
                
                
                    79:39
                    To, lalle ne Jahĩm, ita ce makõma.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:40
                    وَأَمَّا مَنْ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِۦ وَنَهَى ٱلنَّفْسَ عَنِ ٱلْهَوَىٰ
                
                
                
                
                
                    79:40
                    Kuma, amma wanda ya ji tsõron tsayi a gaba ga Ubangijinsa, kuma ya kange kansa daga son rai.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:41
                    فَإِنَّ ٱلْجَنَّةَ هِىَ ٱلْمَأْوَىٰ
                
                
                
                
                
                    79:41
                    To, lalle ne Aljanna ita ce makõma.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:42
                    يَسْـَٔلُونَكَ عَنِ ٱلسَّاعَةِ أَيَّانَ مُرْسَىٰهَا
                
                
                
                
                
                    79:42
                    Sunã tambayar ka game da sa'a, wai yaushe ne matabbatarta?  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:43
                    فِيمَ أَنتَ مِن ذِكْرَىٰهَآ
                
                
                
                
                
                    79:43
                    Me ya haɗã ka da ambatonta?  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:44
                    إِلَىٰ رَبِّكَ مُنتَهَىٰهَآ
                
                
                
                
                
                    79:44
                    Zuwa ga Ubangijinka ƙarshen al'amarinta yake.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:45
                    إِنَّمَآ أَنتَ مُنذِرُ مَن يَخْشَىٰهَا
                
                
                
                
                
                    79:45
                    Kai mai gargaɗi kawai ne ga mai tsõron ta.  - Abubakar Gumi (Hausa)
                
                
                
                
                
                    79:46
                    كَأَنَّهُمْ يَوْمَ يَرَوْنَهَا لَمْ يَلْبَثُوٓا۟ إِلَّا عَشِيَّةً أَوْ ضُحَىٰهَا
                
                
                
                
                
                    79:46
                    Kamar sũ a rãnar da zã su gan ta, ba su zauna ba fãce a lõkacin marẽce ko hantsinsa.  - Abubakar Gumi (Hausa)