Selected

Original Text
Abubakar Gumi

Available Translations

79 An-Nāzi`āt ٱلنَّازِعَات

< Previous   46 Āyah   Those who drag forth      Next >  

بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
In the name of Allah, Most Gracious, Most Merciful.

79:1 وَٱلنَّـٰزِعَـٰتِ غَرْقًا
79:1
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ina rantsuwa da mala'iku mãsu fisgar rãyuka (na kafirai) da ƙarfi.

79:2 وَٱلنَّـٰشِطَـٰتِ نَشْطًا
79:2
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da mãsu ɗibar rãyuka (na mũminai) da sauƙi a cikin nishãɗi.

79:3 وَٱلسَّـٰبِحَـٰتِ سَبْحًا
79:3
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da mãsu sauka daga sama da umurnin Allah kamar suna iyo.

79:4 فَٱلسَّـٰبِقَـٰتِ سَبْقًا
79:4
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan, su zama mãsu gaugãwa (da umurnin Allah) kamar suna tsẽre.

79:5 فَٱلْمُدَبِّرَٰتِ أَمْرًا
79:5
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa, an nan, su kasance masu shirya gudanar da umurni.

79:6 يَوْمَ تَرْجُفُ ٱلرَّاجِفَةُ
79:6
Abubakar Gumi (Hausa) :
Rãnar da mai girgiza abũbuwa (bũsar farko) zã ta kaɗa.

79:7 تَتْبَعُهَا ٱلرَّادِفَةُ
79:7
Abubakar Gumi (Hausa) :
Mai biyar ta (bũsa ta biyu) nã biye.

79:8 قُلُوبٌ يَوْمَئِذٍ وَاجِفَةٌ
79:8
Abubakar Gumi (Hausa) :
Wasu zukãta, a rãnar nan, mãsu jin tsõro ne.

79:9 أَبْصَـٰرُهَا خَـٰشِعَةٌ
79:9
Abubakar Gumi (Hausa) :
Alhãli idãnunsu na ƙasƙantattu.

79:10 يَقُولُونَ أَءِنَّا لَمَرْدُودُونَ فِى ٱلْحَافِرَةِ
79:10
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sunã cẽwa "Ashe lalle zã a iya mayar da mu a kan sãwunmu?

79:11 أَءِذَا كُنَّا عِظَـٰمًا نَّخِرَةً
79:11
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Ashe, idan muka zama ƙasusuwa rududdugaggu?"

79:12 قَالُوا۟ تِلْكَ إِذًا كَرَّةٌ خَاسِرَةٌ
79:12
Abubakar Gumi (Hausa) :
Suka ce: "Waccan kam kõmãwa ce, tãɓaɓɓiya!"

79:13 فَإِنَّمَا هِىَ زَجْرَةٌ وَٰحِدَةٌ
79:13
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, ita kam, tsãwa guda kawai ce.

79:14 فَإِذَا هُم بِٱلسَّاهِرَةِ
79:14
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai kawai gã su a bãyan ƙasa.

79:15 هَلْ أَتَىٰكَ حَدِيثُ مُوسَىٰٓ
79:15
Abubakar Gumi (Hausa) :
Shin, lãbãrin Mũsã ya zo maka?

79:16 إِذْ نَادَىٰهُ رَبُّهُۥ بِٱلْوَادِ ٱلْمُقَدَّسِ طُوًى
79:16
Abubakar Gumi (Hausa) :
A lõkacin da Ubangijinsa Ya kirãye shi, a cikin kwari mai tsarki, wato Duwã?

79:17 ٱذْهَبْ إِلَىٰ فِرْعَوْنَ إِنَّهُۥ طَغَىٰ
79:17
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ka tafi zuwa ga Fir'auna, lalle ne shi, ya ƙẽtare haddi.

79:18 فَقُلْ هَل لَّكَ إِلَىٰٓ أَن تَزَكَّىٰ
79:18
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Sai ka ce masa, Kõ zã ka so ka tsarkaka.

79:19 وَأَهْدِيَكَ إِلَىٰ رَبِّكَ فَتَخْشَىٰ
79:19
Abubakar Gumi (Hausa) :
"Kuma in shiryar da kai zuwa ga Ubangijinka domin ka ji tsoronSa?"

79:20 فَأَرَىٰهُ ٱلْـَٔايَةَ ٱلْكُبْرَىٰ
79:20
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai ya nũna masa ãyar nan mafi girma.

79:21 فَكَذَّبَ وَعَصَىٰ
79:21
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai ya ƙaryata, kuma ya sãɓa (umurni),

79:22 ثُمَّ أَدْبَرَ يَسْعَىٰ
79:22
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sa'an nan ya jũya bãya, yanã tafiya da sauri.

79:23 فَحَشَرَ فَنَادَىٰ
79:23
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai ya yi gayya, sa'an nan ya yi kira.

79:24 فَقَالَ أَنَا۠ رَبُّكُمُ ٱلْأَعْلَىٰ
79:24
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sai ya ce: "Nĩ ne Ubangijinku mafi ɗaudaka."

79:25 فَأَخَذَهُ ٱللَّهُ نَكَالَ ٱلْـَٔاخِرَةِ وَٱلْأُولَىٰٓ
79:25
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sabõda haka Allah Ya kama shi, dõmin azãbar maganar ƙarshe da ta farko.

79:26 إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَعِبْرَةً لِّمَن يَخْشَىٰٓ
79:26
Abubakar Gumi (Hausa) :
Lalle ne, a cikin wannan haƙiƙa akwai abin kula ga wanda yake tsõron Allah.

79:27 ءَأَنتُمْ أَشَدُّ خَلْقًا أَمِ ٱلسَّمَآءُ ۚ بَنَىٰهَا
79:27
Abubakar Gumi (Hausa) :
Shin, kũ ne mafi wuyar halitta ko sama? Allah Ya gina ta.

79:28 رَفَعَ سَمْكَهَا فَسَوَّىٰهَا
79:28
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ya ɗaukaka rufinta, sa'an nan Ya daidaita ta.

79:29 وَأَغْطَشَ لَيْلَهَا وَأَخْرَجَ ضُحَىٰهَا
79:29
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma Ya duhuntar da darenta, kuma Ya fitar da hantsinta.

79:30 وَٱلْأَرْضَ بَعْدَ ذَٰلِكَ دَحَىٰهَآ
79:30
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma, ƙasa a bayan haka Ya mulmula ta.

79:31 أَخْرَجَ مِنْهَا مَآءَهَا وَمَرْعَىٰهَا
79:31
Abubakar Gumi (Hausa) :
Ya fitar da ruwanta daga gare ta da makiyãyarta.

79:32 وَٱلْجِبَالَ أَرْسَىٰهَا
79:32
Abubakar Gumi (Hausa) :
Da duwatsu, Yã kafe ta.

79:33 مَتَـٰعًا لَّكُمْ وَلِأَنْعَـٰمِكُمْ
79:33
Abubakar Gumi (Hausa) :
Domin jiyarwa dãɗi a gare ku, kuma ga dabbõbinku.

79:34 فَإِذَا جَآءَتِ ٱلطَّآمَّةُ ٱلْكُبْرَىٰ
79:34
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, idan uwar masĩfu, mafi girma, ta zo.

79:35 يَوْمَ يَتَذَكَّرُ ٱلْإِنسَـٰنُ مَا سَعَىٰ
79:35
Abubakar Gumi (Hausa) :
Rãnar da mutum zai yi tunãnin abin da ya aikata.

79:36 وَبُرِّزَتِ ٱلْجَحِيمُ لِمَن يَرَىٰ
79:36
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma, a bayyana Jahĩm ga mai gani.

79:37 فَأَمَّا مَن طَغَىٰ
79:37
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, amma wanda ya yi girman kai.

79:38 وَءَاثَرَ ٱلْحَيَوٰةَ ٱلدُّنْيَا
79:38
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma, ya zãɓi rãyuwa ta kusa, (wato dũniya).

79:39 فَإِنَّ ٱلْجَحِيمَ هِىَ ٱلْمَأْوَىٰ
79:39
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, lalle ne Jahĩm, ita ce makõma.

79:40 وَأَمَّا مَنْ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِۦ وَنَهَى ٱلنَّفْسَ عَنِ ٱلْهَوَىٰ
79:40
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kuma, amma wanda ya ji tsõron tsayi a gaba ga Ubangijinsa, kuma ya kange kansa daga son rai.

79:41 فَإِنَّ ٱلْجَنَّةَ هِىَ ٱلْمَأْوَىٰ
79:41
Abubakar Gumi (Hausa) :
To, lalle ne Aljanna ita ce makõma.

79:42 يَسْـَٔلُونَكَ عَنِ ٱلسَّاعَةِ أَيَّانَ مُرْسَىٰهَا
79:42
Abubakar Gumi (Hausa) :
Sunã tambayar ka game da sa'a, wai yaushe ne matabbatarta?

79:43 فِيمَ أَنتَ مِن ذِكْرَىٰهَآ
79:43
Abubakar Gumi (Hausa) :
Me ya haɗã ka da ambatonta?

79:44 إِلَىٰ رَبِّكَ مُنتَهَىٰهَآ
79:44
Abubakar Gumi (Hausa) :
Zuwa ga Ubangijinka ƙarshen al'amarinta yake.

79:45 إِنَّمَآ أَنتَ مُنذِرُ مَن يَخْشَىٰهَا
79:45
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kai mai gargaɗi kawai ne ga mai tsõron ta.

79:46 كَأَنَّهُمْ يَوْمَ يَرَوْنَهَا لَمْ يَلْبَثُوٓا۟ إِلَّا عَشِيَّةً أَوْ ضُحَىٰهَا
79:46
Abubakar Gumi (Hausa) :
Kamar sũ a rãnar da zã su gan ta, ba su zauna ba fãce a lõkacin marẽce ko hantsinsa.